Home Labarai Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta damka daliban da aka kubutar hannun iyayensu

Gwamnatin jihar Kebbi ta mika daliban makarantar ‘yan mata ta Maga da aka kubutar daga hannu ýan bindiga su 24 ga iyayensu.

Wannan dai ya gudana ne bayan wani kwarya-kwaryar biki da aka gudanar, wanda yake cike da adduóin neman zaman lafiya da ingantaccen tsaro a birnin kebbi, wanda gwamantin jihar ta shirya domin sake hada yaran da iyayen nasu.

Bikin ya gudana ne karkashin kulawar kwamishin ilimi ta jihar Hajiya Halima Bande, wadda ta nuna damuwarta bisa halin da yaran da iyayen su suka shiga na tashin hankali.

Da take jawabi a wajen taron matar gwamnan jihar Hajiya Zainab Nasare Idris ta bukaci iyayen yaran da kada wannan dalilin yasa su yi watsa da yin karantun ‘ya’ya mata wanda hakan ka iya mayar da hannun agogo baya.

A makon jiya ne aka tashi da labarin cewa ‘yan bindiga dauke da muggan makamai sun yi awun gaba da ɗaliban sakandiren Maga su 25 a yankin  karamar hukumar Danko-Wasagu da ke jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu a makarantar.

Ana tsaka da jimamin satar ɗaliban kwatsam sai aka tashi kuma da labarin garkuwa da ɗalibai sama da 250  a makarantar sakandiren St Mary da ke garin Kwantagora na jihar Neja.

Baya ga waɗannan, masu ɗauke da makaman sun gudanar da mabanbantan hare-hare tare da awun gaba da mutane a jihohin Kwara da Sokoto da kuma Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp