Home Labarai Tinubu ya ƙara yawan sabbin ƴansandan da za’a ɗauka zuwa 50,000

Tinubu ya ƙara yawan sabbin ƴansandan da za’a ɗauka zuwa 50,000

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa dokar ta ɓaci a ɓangaren tsaro, inda ya buƙaci ɗaukar sabbin sojoji da ƴansanda domin inganta harkar tsaron.

Sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta sanar, mai ɗauke da sanya hannun Bayo Onanuga, ta ce shugaban ya bada umarnin ɗaukar ƙarin sabbin ƴansanda 20,000, wato ƙari a kan 30,000 da ya ce a ɗauka a makon jiya, abinda ya kawo sabon adadin zuwa 50,000.

Tinubu ya kuma bada umarnin amfani da wuraren horar da sabbin jami’an da za’a ɗauka a cibiyoyin horar da masu yiwa ƙasa hidima na NYSC, baya ga cibiyoyin horar da ƴansandan da ake yiwa gyarar fuska domin inganta su.

Sanarwar ta ƙara da cewar, za’a sake horar da jami’an ƴansanda da aka janye daga gadin fitattun mutane kafin mayar da su aikin ɗansandan gada gadan.

Shugaban ƙasar ya kuma bada umarni ga hukumar tsaron farin kaya ta DSS da ta gabatar da mutanen da aka yiwa horo a matsayin dakarun Gandun Daji domin fara aiki nan take, domin kawar da ɓatagarin da suka mamaye wasu dazukan ƙasar.

Tinubu wanda ya bayyana matakin a matsayin na dokar ta ɓaci, ya ce za su ɗuki duk matakan da suka dace wajen baza jami’an tsaro a ko ina, musamman yankunan da ake fama da matsalar tsaro domin tinkarar rikicin kai tsaye, ta yadda za su hana bacci ga duk wani ɗan ta’adda.

Shugaban ya yi amfani da damar wajen jinjinawa hukumomin tsaro wajen kuɓutar da mutane 34 da aka sace a Mujami’ar Kwara da ɗalibai 24 da aka sace a makarantar jihar Kebbi, yayin da ya ce suna ɗaukar matakan da suka dace wajen kuɓutar da ɗaliban makarantar mabiya ɗarikar Katolika dake jihar Neja.

Tinubu ya jinjinawa rundunar sojin ƙasar a kan gudumawar da jami’anta ke bayarwa da kuma gabatar da ta’aziyar rasuwar Janar Musa Uba da ƴanta’adda suka yiwa kisan gilla, yayin da ya buƙace su da su ƙara ƙaimi wajen tabbatar da tsaro a yankunan da ake fama da tashin hankali.

Shugaban ya buƙaci majalisar ƙasa da ta sake fasalin dokokin tsaro domin bai wa jihohi damar samar da ƴansanda na kashin kan su, yayin da ya ce gwamnatin tarayya za ta taimaka musu.

Tinubu ya kuma buƙaci Masallatai da Mujami’u da su dinga neman taimakon jami’an tsaro a duk lokacin da za su gudanar da taron ibadun su, musamman a yankunan da ake fama da matsalar tsaro.

Shugaban ya kuma jajantawa gwamnatoci da kuma mutanen jihohin Kebbi da Borno da Zamfara da Neja da Yobe da kuma Kwara saboda kisan gillar da ƴan ta’adda suka yiwa mutanen su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp