Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da...

Sojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a Adamawa

Dakarun sojojin Najeriya karkashin Operation HADIN KAI sun sami wannan nasara ne sakamakon wani sumame da suka kai domin dakile ayyukan mayaƙan Boko Haram a yankin Arewa maso gabashin Ƙasar.

A sumamen sun sami nasarar hallaka mayakan ƙungiyar Boko Haram biyu ciki harda kwamandanta Abdullahi Mafa, wanda ya jima yana jagorantar hare- hare a yankin Madagali

Wata majiyar tsaro ta shaida cewa da misalin karfe 5:30am ranar Alhamis sojojin haɗin gwiwa da Jami’an bijilanti da mafarauta suka aikawa mabiyan ƴan ta’addan kusa da kogin Visil a karamar hukumar Mafarki dake jihar.

Haka kuma dakarun sun tasamma tashar mota ta Madagali da misalin karfe 6:30 inda suka kama wani mutum mai kimanin shekaru 64 mai suna Dauda Usman wanda ke matsayin mai sayarwa da ƴan Boko Haram jirgi maras matuka wai Done da wasu kayayyakin amfanin yau da kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp