Home Labarai Hisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a Kano

Hisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a Kano

Hukumar Hisbah a jihar Kano ta ce jami’anta sun kama wasu mutum tara Musulmai a jiya Laraba a take ranar farko ta azumin watan Ramadan saboda an gan su suna cin abinci da tsakar rana.

Jihar Kano na da yawan Musulmai, inda tsarin shari’ar Musulunci ke aiki tare da dokokin ƙasa na yau da kullum.

A kowane Ramadan, Hisbah na bincika wuraren sayar da abinci da kasuwanni domin tabbatar da cewa Musulmai na bin dokokin azumi.

A wasu wurare, wurarern cin abinci na ci gaba da aiki musamman a yankunan da Kiristoci da dama ke zaune.

Ga Musulmai masu azumi, cin abinci daga fitowar rana zuwa faduwar rana haramun ne.

Yin azumi na daga cikin ginshikan Musulunci guda biyar da ke kafa yadda Musulmai ke gudanar da rayuwarsu.

Mujahid Aminudeen, mataimakin kwamandan Hisbah, ya shaida wa BBC cewa daga cikin wadanda aka kama akwai mata biyu da maza bakwai.

Ya ce: “Mun kama su kuma suna tare da mu inda za mu koya musu muhimmancin azumi, yadda za su yi salla da karanta Al-Qur’ani, kuma su zama Musulmai nagari.”

Ba a bayyana lokacin da Hisbah za ta saki wadanda aka kama ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp