Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta dakatar da shirin saukewa daga mukami Gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakinsa, Ngozi Odu, bayan tsoma bakin Shugaban Kasa, Bola Tinubu.
Read Also:
Majalisar ta ɗauki matakin dakatar da shirin tsige gwamnan ne a ranar Alhamis, yayin zaman da aka ci gaba da gudanarwa a birnin Port Harcourt, babban birnin jihar.
Tun daga farkon wannan shekara ne wasu ‘yan majalisar suka fara magana kan yiwuwar tsige gwamnan saboda zarge-zarge kan yadda wasu ayyukan gwamnati ke tafiya da kuma rikice-rikicen siyasa a jihar.












