Home Labarai Masu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

Masu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

Aƙalla masu haƙar ma’adinai 33 ne suka mutu sakamakon shakar iskar gas ta sinadarin carbon wace take guba mai ƙarfi yayin da suke hakar ma’adinai a Jihar Plateau, kamar yadda bbc ta rawaito.

Ana hasashen wannan mummunan lamari ya faru ne kafin fitowar rana a wani wuri a wajen garin Wase, wanda kamfanin ma’adinai na Solid Unity Nigeria Ltd, ke gudanarwa.

Ana ganin cewa guba mai ƙarfi ta sinadarin ta taru a cikin ramin ƙasa da iska ba ta samun shiga sosai, wanda ya sa ma’aikatan suka fadi a kasa kafin su kammala aikin dare.

Wadanda suka je aiki da safe ne suka tarar da gawawwakin.

Jami’an tsaro sun rufe wurin hakar ma’adinan, wanda ke kimanin kilomita 200 daga gabas zuwa kudu maso gabas na Jos, babban birnin Jihar Plateau, yayin da ake gudanar da bincike domin gano musabbabin zubar sinadarin.

Hukumomin jihar har yanzu ba su kai ziyara wurin ba, kuma rahotanni sun nuna cewa an samu cikkas wajen kai taimakon gaggawa saboda rashin tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp