Home Labarai Masu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

Masu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

Aƙalla masu haƙar ma’adinai 33 ne suka mutu sakamakon shakar iskar gas ta sinadarin carbon wace take guba mai ƙarfi yayin da suke hakar ma’adinai a Jihar Plateau, kamar yadda bbc ta rawaito.

Ana hasashen wannan mummunan lamari ya faru ne kafin fitowar rana a wani wuri a wajen garin Wase, wanda kamfanin ma’adinai na Solid Unity Nigeria Ltd, ke gudanarwa.

Ana ganin cewa guba mai ƙarfi ta sinadarin ta taru a cikin ramin ƙasa da iska ba ta samun shiga sosai, wanda ya sa ma’aikatan suka fadi a kasa kafin su kammala aikin dare.

Wadanda suka je aiki da safe ne suka tarar da gawawwakin.

Jami’an tsaro sun rufe wurin hakar ma’adinan, wanda ke kimanin kilomita 200 daga gabas zuwa kudu maso gabas na Jos, babban birnin Jihar Plateau, yayin da ake gudanar da bincike domin gano musabbabin zubar sinadarin.

Hukumomin jihar har yanzu ba su kai ziyara wurin ba, kuma rahotanni sun nuna cewa an samu cikkas wajen kai taimakon gaggawa saboda rashin tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp