Home Labarai Sojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi...

Sojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Najeriya ta bakin kakakin ma’aikatar tsaronta ta tabbatar da isowar sojojin Amurka aƙalla 100 cikin ƙasar ta yammacin Afrika don taimaka mata a yaƙin da ta ke da ƴan ta’addar da ke kaiwa jama’a hare-hare.

Kakakin shalkwatar tsaron Najeriyar Manjo Janar Samaila Uba ya ce tabbas sojojin Amurkan sun shiga Najeriyar amma ba za su shiga fagen daga don yin yaƙi ba, face aikin horar da dakarun Najeriyar dabarun yaƙi da ƴan ta’addan.

Isowar sojojin Amurka na zuwa bayan tun farko Donald Trump ya zargi Najeriyar da gazawa wajen baiwa Kiristoci kariya daga hare-haren da ƴanta’addan da ya kira da Musulmai ke kaiwa a sassan ƙasar.

Sai dai tuni gwamnatin Najeriya ta musanta wannan zargin bayan da ta ce ƴan ta’addan na kashe dukkanin ɓangarorin Musulmai da kuma Kiristoci kuma dakarunta na aiki tuƙuru wajen yaƙi da su musamman a yankin arewa maso yammaci da kuma arewa maso gabas.

Amurkan ta kai hare-hare cikin watan Disamba kan yankunan da ta ce a nan ne mayaƙan IS suke a yankin na arewa maso yammacin Najeriyar kuma tun daga wancan lokaci bayanai ke cewa akwai sojojin na Washington da jiragen yaƙinta da ke shawagi a sassan Najeriyar don yaƙi da matsalolin tsaron.

Cikin kwanakin baya-bayan nan anga tarin jiragen yaƙin Amurka ɗauke da ko dai sojoji ko kuma makamai na isa sassan jihohin arewacin ƙasar kamar yadda bayanan bin diddigin da kafar Reuters ke yi suka bayyana.

Tun a farkon watan nan ma’aikatar tsaron Najeriyar ta ce tana tsammanin isowar ƙarin Sojin Amurka 200 zuwa ƙasar.

Najeriya mai yawan jama’a fiye da miliyan 240 na da rinjaye mabiyan addinin Islama ne a yankin arewaci yayinda mabiya addinin Kirista ke a yankin kudanci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp