Home Labarai Sojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi...

Sojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Najeriya ta bakin kakakin ma’aikatar tsaronta ta tabbatar da isowar sojojin Amurka aƙalla 100 cikin ƙasar ta yammacin Afrika don taimaka mata a yaƙin da ta ke da ƴan ta’addar da ke kaiwa jama’a hare-hare.

Kakakin shalkwatar tsaron Najeriyar Manjo Janar Samaila Uba ya ce tabbas sojojin Amurkan sun shiga Najeriyar amma ba za su shiga fagen daga don yin yaƙi ba, face aikin horar da dakarun Najeriyar dabarun yaƙi da ƴan ta’addan.

Isowar sojojin Amurka na zuwa bayan tun farko Donald Trump ya zargi Najeriyar da gazawa wajen baiwa Kiristoci kariya daga hare-haren da ƴanta’addan da ya kira da Musulmai ke kaiwa a sassan ƙasar.

Sai dai tuni gwamnatin Najeriya ta musanta wannan zargin bayan da ta ce ƴan ta’addan na kashe dukkanin ɓangarorin Musulmai da kuma Kiristoci kuma dakarunta na aiki tuƙuru wajen yaƙi da su musamman a yankin arewa maso yammaci da kuma arewa maso gabas.

Amurkan ta kai hare-hare cikin watan Disamba kan yankunan da ta ce a nan ne mayaƙan IS suke a yankin na arewa maso yammacin Najeriyar kuma tun daga wancan lokaci bayanai ke cewa akwai sojojin na Washington da jiragen yaƙinta da ke shawagi a sassan Najeriyar don yaƙi da matsalolin tsaron.

Cikin kwanakin baya-bayan nan anga tarin jiragen yaƙin Amurka ɗauke da ko dai sojoji ko kuma makamai na isa sassan jihohin arewacin ƙasar kamar yadda bayanan bin diddigin da kafar Reuters ke yi suka bayyana.

Tun a farkon watan nan ma’aikatar tsaron Najeriyar ta ce tana tsammanin isowar ƙarin Sojin Amurka 200 zuwa ƙasar.

Najeriya mai yawan jama’a fiye da miliyan 240 na da rinjaye mabiyan addinin Islama ne a yankin arewaci yayinda mabiya addinin Kirista ke a yankin kudanci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp