Home Labarai Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin...

Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8

Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin kuɗi naira biliyan 5 domin rage raɗaɗin mummunar gobarar da ta ƙone kasuwar bayan wata gobara da ta tashi a cikin kasuwar.

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ne ya jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano wadda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aika jihar domin jajantawa waɗanda ibtila’in gobarar ya shafa.

A lokacin da yake jawabi cikin dandazon ƴan kasuwar Kashim Shettima ya jajantawa ƴan jama’a tare da sanar da tallafin da gwamnatin tarayya ta bai wa ƴan kasuwar na Naira biliyan 5.

Shettima ya ce gwamnonin jam’iyyar APC 29 sun bada tallafin naira biliyan 3 ga wadanda suka tafka wannan asara, inda ya ce za su miƙa jimillar kuɗi naira biliyan 8 ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf domin a hada kwamitin da za a tallafawa ƴan kasuwar.

“Bugu da ƙari, gwamnoninmu na APC guda 29 suma sun kawo tallafin biliyan 3. A taƙaice jama’a, Insha Allah za mu damƙawa gwamnan jihar Kano naira biliyan 8, zai haɗa kwamiti”

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ya ce Kano ita ce cibiyar Arewa don haka za su haɗa hannu domin ganin cewa sun ceto al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp