Home Labarai Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin...

Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8

Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin kuɗi naira biliyan 5 domin rage raɗaɗin mummunar gobarar da ta ƙone kasuwar bayan wata gobara da ta tashi a cikin kasuwar.

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ne ya jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano wadda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aika jihar domin jajantawa waɗanda ibtila’in gobarar ya shafa.

A lokacin da yake jawabi cikin dandazon ƴan kasuwar Kashim Shettima ya jajantawa ƴan jama’a tare da sanar da tallafin da gwamnatin tarayya ta bai wa ƴan kasuwar na Naira biliyan 5.

Shettima ya ce gwamnonin jam’iyyar APC 29 sun bada tallafin naira biliyan 3 ga wadanda suka tafka wannan asara, inda ya ce za su miƙa jimillar kuɗi naira biliyan 8 ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf domin a hada kwamitin da za a tallafawa ƴan kasuwar.

“Bugu da ƙari, gwamnoninmu na APC guda 29 suma sun kawo tallafin biliyan 3. A taƙaice jama’a, Insha Allah za mu damƙawa gwamnan jihar Kano naira biliyan 8, zai haɗa kwamiti”

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ya ce Kano ita ce cibiyar Arewa don haka za su haɗa hannu domin ganin cewa sun ceto al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp