Home Labarai Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Ƙungiyar Kwankwasiyya a jihar Kano ta mayar da martani kan ƙudurin da wasu mambobin majalisar wakilan Amurka suka gabatar na a hukunta jagoranta Musa Kwankwaso dangane da zargin musguna wa Kiristoci a Najeriya.

A cikin wata sanarwar da ta fitar, ƙungiyar ta ce “duk da cewa tana sane da muhimmancin damuwar ƙasashen duniya kan batutuwan haƙƙin dan’adam da ‘yancin addini, amma kuma Najeriya ta kasance ƙasa mai yalwar al’adu da addinai, kuma tana fuskantar matsalolin tsaro masu sarƙaƙiya da ke shafar kowane ɓangare ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba.”

A ranar Laraba ne wasu ‘yan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da ƙuduri a zauren majalisar suna bukatar a sanya takunkumi kan Kwankwaso da wasu kungiyoyi da suka kira na “‘yan bindiga” wadanda suka zarga da taimakawa wajen cusguna wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Sai dai kungiyar ta Kwankwasiyya ta bayyana Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan kasa.

Ta ce “yana da goyon bayan al’ummomin addinai daban daban, kuma a kullum yana inganta juriya da fahimtar juna tsakanin mabambantan ɓangarori.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp