Home Labarai Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Ƙungiyar Kwankwasiyya a jihar Kano ta mayar da martani kan ƙudurin da wasu mambobin majalisar wakilan Amurka suka gabatar na a hukunta jagoranta Musa Kwankwaso dangane da zargin musguna wa Kiristoci a Najeriya.

A cikin wata sanarwar da ta fitar, ƙungiyar ta ce “duk da cewa tana sane da muhimmancin damuwar ƙasashen duniya kan batutuwan haƙƙin dan’adam da ‘yancin addini, amma kuma Najeriya ta kasance ƙasa mai yalwar al’adu da addinai, kuma tana fuskantar matsalolin tsaro masu sarƙaƙiya da ke shafar kowane ɓangare ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba.”

A ranar Laraba ne wasu ‘yan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da ƙuduri a zauren majalisar suna bukatar a sanya takunkumi kan Kwankwaso da wasu kungiyoyi da suka kira na “‘yan bindiga” wadanda suka zarga da taimakawa wajen cusguna wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Sai dai kungiyar ta Kwankwasiyya ta bayyana Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan kasa.

Ta ce “yana da goyon bayan al’ummomin addinai daban daban, kuma a kullum yana inganta juriya da fahimtar juna tsakanin mabambantan ɓangarori.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp