Home Labarai Sojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a Borno

Sojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun daƙile wani hari da mayaƙan ISWAP suka kai kan sansanin sojin Auno a Borno, sannan suka kaddamar da harin ramuwar gayya wacce ta lalata kayan yaƙi da dabarun ‘yan ta’addan.

Rundunar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da ta fitar wa manema labarai.

Sanarwar ta ce “A daren 5 ga Fabrairun 2026, mayaƙan ISWAP sun kai hari kan wani sansanin sojoji amma Sojojin sun dakile harin cikin tsari da ƙwarewa.”

Bayan daƙile harin, a ranar 9 ga Fabrairu, sojojin tare da hadin gwiwar dakarun sa kai ta CJTF suka ƙaddamar da samame ta ramuwar gayya a kan mayaƙan ISWAP ɗin a layin Komala da ke ƙaramar hukumar Konduga.

A yayin samamen, sojojin sun kashe mayaƙan Iswap 16, yayin da sauran suka tsere da raunuka masu tsanani.

Haka kuma, sojojin sun ƙwato fiye da kekuna 20 da kayayyakin yaƙi da dama da makamai da sauran kayan amfani na ‘yan ta’adda.

Sojojin sun kuma kama wasu mutane da ake zargin suna tura ƙwayoyi da sauran kayan aiki don taimakawa ayyukan ISWAP a yankin Bukarti.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp