Home Labarai Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Tsoho shugaban hukumar kula da aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Sheikh Abdullah Saleh Usman, ya bayyana dalilan da suka sanya shi ya ajiye aiki a matsayin shugaban hukumar, wanda ya fara aiki daga ranar Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.

A wata sanarwa da ya fitar wadda da ya sanyawa hannu da kansa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa murabus ɗin nasa ya biyo bayan dalilai na kansa, bayan yin dogon tunani, addu’a da shawarwari da iyalansa.

Ya jaddada cewa matakin nasa ba shi da alaƙa da wata matsala ko rashin jituwa da Gwamnatin Tarayya ko hukumar NAHCON.

Tsohon shugaban NAHCON ya tabbatar da cewa ya miƙa takardar murabus ɗinsa a rubuce ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar NAHCON ta shekarar 2006 ya tanada.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa amincewa da damar da ya ba shi na yi wa ƙasa da al’ummar Musulmi hidima, tare da yabawa Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima kan shawarwari da goyon bayan da ya ba shi.

Haka kuma, ya miƙa godiya ga Mambobin Kwamitin Gudanarwa, ma’aikata da shugabannin sassan hukumar, yana mai yaba jajircewa da sadaukarwarsu wajen inganta aikin Hajjin Najeriya.

Ya kuma gode wa Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, Kamfanonin Hajji, Kamfanonin Jiragen Sama da hukumomin Saudiyya bisa kyakkyawan haɗin gwiwa.

A ƙarshe, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya yi addu’ar Allah Ya karɓi ayyukan da aka gudanar, Ya jagoranci sabon shugabancin NAHCON, tare da roƙon Allah ya sa alhazan Najeriya su yi Hajji karɓaɓɓe (Hajj Mabrur)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp