Home Labarai Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Tsoho shugaban hukumar kula da aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Sheikh Abdullah Saleh Usman, ya bayyana dalilan da suka sanya shi ya ajiye aiki a matsayin shugaban hukumar, wanda ya fara aiki daga ranar Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.

A wata sanarwa da ya fitar wadda da ya sanyawa hannu da kansa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa murabus ɗin nasa ya biyo bayan dalilai na kansa, bayan yin dogon tunani, addu’a da shawarwari da iyalansa.

Ya jaddada cewa matakin nasa ba shi da alaƙa da wata matsala ko rashin jituwa da Gwamnatin Tarayya ko hukumar NAHCON.

Tsohon shugaban NAHCON ya tabbatar da cewa ya miƙa takardar murabus ɗinsa a rubuce ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar NAHCON ta shekarar 2006 ya tanada.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa amincewa da damar da ya ba shi na yi wa ƙasa da al’ummar Musulmi hidima, tare da yabawa Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima kan shawarwari da goyon bayan da ya ba shi.

Haka kuma, ya miƙa godiya ga Mambobin Kwamitin Gudanarwa, ma’aikata da shugabannin sassan hukumar, yana mai yaba jajircewa da sadaukarwarsu wajen inganta aikin Hajjin Najeriya.

Ya kuma gode wa Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, Kamfanonin Hajji, Kamfanonin Jiragen Sama da hukumomin Saudiyya bisa kyakkyawan haɗin gwiwa.

A ƙarshe, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya yi addu’ar Allah Ya karɓi ayyukan da aka gudanar, Ya jagoranci sabon shugabancin NAHCON, tare da roƙon Allah ya sa alhazan Najeriya su yi Hajji karɓaɓɓe (Hajj Mabrur)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp