Home Labarai Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Tsoho shugaban hukumar kula da aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Sheikh Abdullah Saleh Usman, ya bayyana dalilan da suka sanya shi ya ajiye aiki a matsayin shugaban hukumar, wanda ya fara aiki daga ranar Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.

A wata sanarwa da ya fitar wadda da ya sanyawa hannu da kansa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa murabus ɗin nasa ya biyo bayan dalilai na kansa, bayan yin dogon tunani, addu’a da shawarwari da iyalansa.

Ya jaddada cewa matakin nasa ba shi da alaƙa da wata matsala ko rashin jituwa da Gwamnatin Tarayya ko hukumar NAHCON.

Tsohon shugaban NAHCON ya tabbatar da cewa ya miƙa takardar murabus ɗinsa a rubuce ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar NAHCON ta shekarar 2006 ya tanada.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa amincewa da damar da ya ba shi na yi wa ƙasa da al’ummar Musulmi hidima, tare da yabawa Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima kan shawarwari da goyon bayan da ya ba shi.

Haka kuma, ya miƙa godiya ga Mambobin Kwamitin Gudanarwa, ma’aikata da shugabannin sassan hukumar, yana mai yaba jajircewa da sadaukarwarsu wajen inganta aikin Hajjin Najeriya.

Ya kuma gode wa Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, Kamfanonin Hajji, Kamfanonin Jiragen Sama da hukumomin Saudiyya bisa kyakkyawan haɗin gwiwa.

A ƙarshe, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya yi addu’ar Allah Ya karɓi ayyukan da aka gudanar, Ya jagoranci sabon shugabancin NAHCON, tare da roƙon Allah ya sa alhazan Najeriya su yi Hajji karɓaɓɓe (Hajj Mabrur)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp