Home General Gwamnatin Kano ta samu bashin naira biliyan 177 daga Faransa domin samar...

Gwamnatin Kano ta samu bashin naira biliyan 177 daga Faransa domin samar da ruwan sha

Gwamnatin Kano ta samu bashin Naira biliyan 177.4 daga Hukumar Cigaban Faransa wato French Development Agency domin samar da ruwan sha a jihar.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda Kwamishinan Ruwa na jihar, Alhaji Ali Haruna Makoɗa ya wakilta ne ya bayyana hakan a wani taron ƙara wa juna sani na kwanaki biyu da aka yi a Kano domin bibiya da tsara aikace-aikace wanda ya samu halartar wakilai daga jihohin Filato da Enugu da Ondo.

Ya ce aikin na samar da ruwan sha, yana cikin shirin inganta samar da ruwan sha na ƙasa, wanda ya samu sahalewar Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta Najeriya.

Gwamnan ya ce an samu tsaiko ne a kan aikin ne tun bayan ɓarkewar annobar COVID-19 da wasu ƙalubalen, amma ya ƙara da cewa yanzu sun shirya cigaba da aikin, wanda ya ce za a kammala nan da shekara biyu.

Injiniya Garba Ahmad Bichi, Manajan Darakta na Hukumar Gidan Ruwan Kano ya ce aikin ya ƙunshi sake gina sabon hanyar adanawa da gyara ruwa wanda zai ɗauki lita miliyan 250 a kullum, wanda ya ce zai taimaka matuƙa wajen rage matsalar ƙarancin ruwa a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp