Home General An saki yaran da gwamnati ta tuhuma da cin amanar ƙasa

An saki yaran da gwamnati ta tuhuma da cin amanar ƙasa

Wata kotu a Abuja ta soke tare da sakin yaran nan guda 26 tare sauran mutanen da gwamnatin ƙasar ta tuhuma da cin amanar ƙasa a ranar Juma’a.

Ana tuhumar mutanen ne 72 sakamakon zargin su da laifin ɗaga tutar Rasha a lokacin zanga-zangar matsin rayuwa ta #Endbadgovernace a Agusta. Waɗanda ake tuhumar dai sun musanta aika laifin.

Sakin ya biyo bayan umarnin da shugaba Tinubu ya bayar ranar Litinin cewa a sake su sannan kuma a miƙa su ga ma’aikatar jinƙan ƙasar domin kula da walwalarsu sannan ta sada su da mahaifansu tare da binciken dalilin da ya sa aka tsare su na tsawon lokaci alhali yara ne.

Tuni dai an miƙa yaran 26 tare da sauran manya fiye 50 ga ma’aikatar jinƙai.

Tunda farko dai ministan shari’ar Najeriya ya saka baki a batun inda ya nemi a mayar da kyas ɗin ofishinsa domin tabbatar da sakin yaran.

Wasu masu rajin kare haƙƙin ɗan adam sun shaida cewa yaran sun kasance a tsare a hannun ƴansanda tun watan Agusta, wani abu da ke janyo kiraye-kirayen a nema musu haƙƙinsu.

Ɗaya daga cikin iyayen yaran nan da gwamnatin Najeriya ta tuhuma da cin amanar ƙasa sakamakon zanga-zanga kan tsadar rayuwa ta ce ta yi farin ciki da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya ce a sake su.

Kafin ta je Abuja, Fatima ta ce an kira ta an faɗa mata ɗaya daga cikin ‘ya’yan nata ba shi da lafiya. Bayan ta isa kuma, kullum sai ta je wurin da ake tsare da su.

“Tun da na zo Abuja ban koma gida ba, kullum sai na je wajensu. Wani lokacin ma sai na je na yi bara kafin na samu abin da zan kai musu.

“Lokacin da na fara zuwa, da kyar aka bari na ga ɗaya daga cikin yaran nan kuma sai da na ba da kuɗi. Wani lokacin N1,000 ma ba ta isa, korar mu suke yi har sai ka samu masu kirki ne za su ƙyale ka,” kamar yadda ta yi bayani.

Ta ce tun yaran suna ƙanana aurenta da mahaifinsu ya mutu, kuma yana can kwance yana jinya sakamakon cutar shanyewar ɓarin jiki.

Ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta ce kama yaran ya saɓa wa dokokin ‘yancin ɗan’adam na ƙasa da ƙasa, kuma yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sake “nan take ba tare da wani sharaɗi ba”.

Malam Isa Sanusi, shugaban kungiyar a Najeriya, ya bayyana wa BBC cewar sun kuma nemi a biya diyya saboda “gallazawa da galabaitarwa da yaran suka fuskanta tsawon lokacin da ake tsare a cikin watan Agustan”.

Kwana ɗaya bayan sukar da gwamnatin ta sha, Antoni janar kuma babban lauyan gwamnatin Najeriya, Lateef Fagbemi, ya nemi rundunar ‘yansandan ta miƙa masa lamarin domin cigaba da bibiyar shari’ar.

A ƙarshen mako kuma sai ga Ministar Mata Imaan Sulaiman-Ibrahim ta ziyarci yaran, inda aka gan ta a hotuna tana raba musu ruwa da abinci tare da cin alwashin yi musu adalci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp