Home General Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakai kan...

Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakai kan Kangwaye dake jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya ta bukaci gwamnatin jihar da ta umarci masu kangwaye (filayen da ba’a gina ba ko tsofaffin gidajen da ba kowa a ciki) dasu gine ko kuma su sayar da su.

Wannan na zuwa ne bayan kudurin da Dan majalisa mai wakiltar Karamar hukumar Kiru Usman Abubakar Tasiu ya gabatarwa zauren majalisar.

Kiru ya ce yawancin kangwaye da gidajen da baa karasa ba a jihar sun zama wuraren lalata tarbiya da barazanar tsaro.

Da yake bada gudunmuwa akan kudurin dan majalisa mai wakiltar Karamar hukumar Madobi Sulaiman Mukhtar Ishaq ya ce ba iya kangwaye ba, hatta gidajen da aka gina na kwankwasiya da Amana city da Bandirawo sun zama barazanar tsaro da tarbiyyar al’ummar Kano.

Majalisar ta kafa kwamiti domin binciko mata lamuran kangwaye, inda zata mika shi ga gwamnatin Kano domin tabbatar da gyara a al’amarin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp