Home General Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakai kan...

Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakai kan Kangwaye dake jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya ta bukaci gwamnatin jihar da ta umarci masu kangwaye (filayen da ba’a gina ba ko tsofaffin gidajen da ba kowa a ciki) dasu gine ko kuma su sayar da su.

Wannan na zuwa ne bayan kudurin da Dan majalisa mai wakiltar Karamar hukumar Kiru Usman Abubakar Tasiu ya gabatarwa zauren majalisar.

Kiru ya ce yawancin kangwaye da gidajen da baa karasa ba a jihar sun zama wuraren lalata tarbiya da barazanar tsaro.

Da yake bada gudunmuwa akan kudurin dan majalisa mai wakiltar Karamar hukumar Madobi Sulaiman Mukhtar Ishaq ya ce ba iya kangwaye ba, hatta gidajen da aka gina na kwankwasiya da Amana city da Bandirawo sun zama barazanar tsaro da tarbiyyar al’ummar Kano.

Majalisar ta kafa kwamiti domin binciko mata lamuran kangwaye, inda zata mika shi ga gwamnatin Kano domin tabbatar da gyara a al’amarin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp