Home General Gwamnatin Kano za ta tallafawa matasa 3000 da wata kungiya ke koyawa...

Gwamnatin Kano za ta tallafawa matasa 3000 da wata kungiya ke koyawa sana’o’i a Kano – Sani Danja

Mashawarcin gwamnan Kano na musamman kan harkokin matasa da wasanni Sani Musa Danja ya sha alwashin hada kai da Kungiyoyi masu zaman kasansu don inganta rayuwar matasan jihar.

” Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya damu matuka da rayuwar matasa , shi yasa gwamnatinsa ta fi mai da hankali wajen tallafawa mata da matasa don inganta rayuwarsu, da ta al’umma baki daya”.

Alhaji Sani Danja ya bayyana hakan ne lokacin da ya kai ziyarar ganin yadda ake koyawa matasa 3000 sana’o’i daban-daban wanda wata kungiya mai suna 9ja food fiesta ya dauki nauyi a Kano.

Sani Danja ya baiwa matasan tabbacin gwamnatin jihar Kano zata tallafawa matasa da kayan aikin sana’o’in da suka koya ko jari, don tabbatar da cewa al’ummar Kano sun amfana da ilimin da suka koya.

Ya ce kofar ofishinsa a bude take don hada kai da duk wata kungiya mai son ganin ta tallafawa rayuwar matasan jihar Kano kamar yadda kungiyar 9ja food fiesta ta yi.

”Tun kafin na zama mai baiwa gwamnan Kano shawara akan harkokin matasa na damu matuka da al’amuran matasa da masu karin karfi domin talakawa da ya’yansu ne suke kallo fina-finai na har na kai matakin da na Kai, yanzu kuma da aikin da gwamna ya doramin , don haka dole na tsaya tsayin daka don ganin an inganta rayuwarku”.

Da yake nasa jawabin shugaban kungiyar 9ja food fiesta Muhammad Mustapha ya ce sun zo jihar Kano ne da nufin koyawa matasa maza da mata 2000 sana’o’i , amma daga bisani suka ga akwai bukatar kara adadin zuwa 3000 .

” Babu shakka wannan Aikin ne don tallafawa rayuwar matasan jihar Kano, kamar yadda muka yi a Abuja, amma mun ji dadin yadda mai baiwa gwamnan Kano shawara kan harkokin matasa da wasanni Sani Musa Danja ya ba mu duk wata gudunmawa da muke bukata don ganin an sami nasarar da muka sanya a gaba”.

Muhammad Mustafa ya yi kira ga kamfanoni da masu hannu da shuni a jihar Kano da su shigo cikin shirin don tallafawa matasan da suka gama koyon sana’o’in da jari ko kayan aikin da suka koya, don su dogara da kawunansu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp