Home General PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

Gwamnonin babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya sun nisanta kansu da yunƙurin haɗaka tsakanin jam’iyyarsu da wasu jam’iyyun siyasa.

Ƙungiyar gwamnonin ƙarƙashin gwamnan Bauchi Bala Mohammed ta ce ba za ta haɗe da wata jam’iyya ba da nufin tunkarar zaɓen 2027.

“Ba za mu shiga wata haɗaka ba da kowa da nufin tunkarar zaɓen 2027,” kamar yadda ƙungiyar gwamnonin PDP ta bayyana a sanarwar da ta fitar bayan taron da suka gudanar a Ibadan jihar Oyo.

Wannan dai ya ci karo da iƙirarin tsohon ɗantakarar jam’iyyar kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar a kwanakin baya inda ya ce suna yunƙurin ƙulla haɗaka da wasu jam’iyyu.

Sanarwar gwamnonin PDP ya nuna akwai saɓanin ra’ayi tsakanin ɓangarensu da na Atiku Abubakar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp