Home General Tinubu ya magantu kan kisan Bassa ta jihar Filato

Tinubu ya magantu kan kisan Bassa ta jihar Filato

Shugaba Bola Tinubu ya nuna ɓacin-rai da kuma kaɗuwa kan kashe mutane da wasu ƴan bindiga suka yi a ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Filato.

Shugaban ya yi Alla-wadai da lamarin, ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga al’ummar jihar – inda ya buƙaci a nemi hanyar warware rikicin da kuma samar da zaman lafiya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Bayo Onanuga ya fitar, inda Tinubu ya nanata muhimmancin haɗin-kai ba tare da nuna bambacin addini ko kabila.

“Dole ne shugabannin al’ummomi da na addini da kuma siyasa su zo su haɗa-kai don daƙile waɗannan hare-hare da suka addabi jama’a,” in ji Tinbu.

Aƙalla mutum 50 ne suka mutu a harin da ƴan bindigar suka kai jihar a cikin daren Litinin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp