Home General Yajin Aikin ASUU:Hukumar NUC Ta Bada Lasisi Ga Sabbin Jami’o’i 12 A...

Yajin Aikin ASUU:Hukumar NUC Ta Bada Lasisi Ga Sabbin Jami’o’i 12 A Nijeriya

Daidai lokacin da Kungiyar Daliban Jami’oin Nijeriya Ta NANs ke gudanar da zanga zangar kin jinin yajin aikin kungiyar ASUU, Hukumar dake lura da jami’oin kasar ta NUC ta bawa jami’oi 12 masu zaman kansu lasisin gudanarwa.

A kalla dalibai dubu 3 dake gudanar da karatu a jami’oin gwamnatin kasar suka tare manayan hanyoyi a Nijeriya tare da dakatar da zirga-zirgar ababa hawa a jami’ar Nsukka dake jihar Enugu a kudancin Nijeriya saboda yajin aikin na ASUU.

Masu zanga-zangar dai na dauke da kwalaye da rubuce-rubuce kamar “ Muddin ba’a dakatar da yajin aikin ASUU ba, to babu zaben Fidda Gwani na Jam’iyyun Siyasa” “ mung aji da zama a gida” “ ya kamata Gwamnatin tarayya ta sasanta da ASUU, “Muna so Mu Koma makaranta.

Sai dai ana tsaka da wannan dambarwa Ministan Ilimin kasar Malam Adamu Adamu, ya gabatar da lasisin bude wasu sabbin jami’oi masu zaman kan su a kasar.

Sabbin jami’oin da aka mikawa lasisin sun hadar da Pen resources University a jihar Gombe; Al-ansar university a Garin maidugurin Jihar Borno: sai Margeret Lawrence University Galilee dake jihar Delta da kuma Khalifa Isiyaku Rabiu University, a Jihar Kano.

Sauran sun hadar da Sport University, dake Idumuje a jihar Delta sai Baba Ahmad university a jihar Kano sai kuma Saisa university of medical Sciences and technology, a jihar Sokoto da kuma Nigerian British University, dake Asa, a jihar Abia.

Akwai kuma Peter University, dake Achina/Onneh a jihar Aambra; sia Newgate University, Minna” Europena University of Nigeria, dake Duboyi a babban birnin tarayya Abuja sai kuma Northwest University Sokoto dake Jihar Sokoto.

Da yake jawabi a yayin taron mika lasisin ministan ilimin yace, duk cewa adadin jami’oin ka iya yin yawa amma akwai bukatar a samar da Karin jami’o’I a kasar.

“Gwamnati nada masaniya kan bukatarsamar da cigaba ga al’umma, sanina cewa dukkan kasashen da suka cigaba kuma ake lallaon su matsayin kasashe mafi daraja to sun kula da jami’o’in su gani da lura da yawan al’ummar su.

Yakuma ce sabbin jami’o’in zasu kasance suna da alaka da Tsuffin jami’o’in kasar a fannin koyo da koyarwa bisa jagorancin hukumar dake lura dasu ta NUC.

Ya bukaci masu mamallaka jami’oin dasu cigaba da samar da kudade domin inganta makarantun ta hanyar samar da kayan koyo da koyar da kuma baiwa jami’o’in damar karbuwa.

Daga bisani Babban sakataren hukumar dake lura da jami’oin kasar ta NUC Farfesa Abubakar Rasheed ya yabada kokarin wadanda suka samar da jami’o’in a Nijeriya.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp