Home Labarai Buhari ya Bukaci ASUU Ta Kawo Karshen Yajin Aikin Da Take Yi

Buhari ya Bukaci ASUU Ta Kawo Karshen Yajin Aikin Da Take Yi

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bukaci kungiyar malaman Jami’an ta ASUU, da ta kawo karshen yajin aikin da take yi.

Buhari ya yi wannan kira ne wajen biki murnar zagayowar ranar samun albakatun kasa gami da bada lambar yabo da aka gudanar a fadar shugaban dake birnin tarayya Abuja

Buhari ya bukaci kungiyar data janye matakin data dauka na yajin aikin, la’akari da halin da daliban Jami’oin kasar ke ciki sakamakon yajin aikin da suka tsunduma.

Ya kuma bukaci kungiyar Dalibai ta kasa NANs ta kara hakuri, kasancewa gwamnati na kokarin shawo kan matsalar.

Buhari yace ko a ranar daya ga watan Fabreru ya umarci shugaban Ma’aikatan Fadar gwamnatin tarayya Farfesa Ibrahim Gambari, Ministan Kwadago da Ayyuka Chris Ngige, da kuma Ministan Ilimi Adamu Adamu, su san mai yiwuwa wajen ganin an magance matsalar yajin aikin

A ranar litinin din wannan makon kungiyar Malaman Jami’ar ta ASUU ta sanar da kara wa’adin yajin aikin da take zuwa watannin Uku (3).

Kungiyar dai na bukatar wasu makudan kudade domin farfado da jami’oin Gwamnati, gami da samar da tsarin biyan albashi na (UTAS) da kuma wasu bukatu da take nema a wajen gwamnatin tarayya Nijeriyar.

Sauran bukatan sun hadar da cika musu alkawarin da gwamantin tarayyar Nijeriyar tayi a cikin wata takardar da aka sanya hannu a alkawarin kungiyar da Gwamantin tarayya na shekarar 2019, tare da nuna rashin gamsuwa da tsarin biyan Albashin bai day ana IPPIS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp