Home Labarai Buhari ya Bukaci ASUU Ta Kawo Karshen Yajin Aikin Da Take Yi

Buhari ya Bukaci ASUU Ta Kawo Karshen Yajin Aikin Da Take Yi

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bukaci kungiyar malaman Jami’an ta ASUU, da ta kawo karshen yajin aikin da take yi.

Buhari ya yi wannan kira ne wajen biki murnar zagayowar ranar samun albakatun kasa gami da bada lambar yabo da aka gudanar a fadar shugaban dake birnin tarayya Abuja

Buhari ya bukaci kungiyar data janye matakin data dauka na yajin aikin, la’akari da halin da daliban Jami’oin kasar ke ciki sakamakon yajin aikin da suka tsunduma.

Ya kuma bukaci kungiyar Dalibai ta kasa NANs ta kara hakuri, kasancewa gwamnati na kokarin shawo kan matsalar.

Buhari yace ko a ranar daya ga watan Fabreru ya umarci shugaban Ma’aikatan Fadar gwamnatin tarayya Farfesa Ibrahim Gambari, Ministan Kwadago da Ayyuka Chris Ngige, da kuma Ministan Ilimi Adamu Adamu, su san mai yiwuwa wajen ganin an magance matsalar yajin aikin

A ranar litinin din wannan makon kungiyar Malaman Jami’ar ta ASUU ta sanar da kara wa’adin yajin aikin da take zuwa watannin Uku (3).

Kungiyar dai na bukatar wasu makudan kudade domin farfado da jami’oin Gwamnati, gami da samar da tsarin biyan albashi na (UTAS) da kuma wasu bukatu da take nema a wajen gwamnatin tarayya Nijeriyar.

Sauran bukatan sun hadar da cika musu alkawarin da gwamantin tarayyar Nijeriyar tayi a cikin wata takardar da aka sanya hannu a alkawarin kungiyar da Gwamantin tarayya na shekarar 2019, tare da nuna rashin gamsuwa da tsarin biyan Albashin bai day ana IPPIS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp