Home Labarai Buhari ya Bukaci ASUU Ta Kawo Karshen Yajin Aikin Da Take Yi

Buhari ya Bukaci ASUU Ta Kawo Karshen Yajin Aikin Da Take Yi

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bukaci kungiyar malaman Jami’an ta ASUU, da ta kawo karshen yajin aikin da take yi.

Buhari ya yi wannan kira ne wajen biki murnar zagayowar ranar samun albakatun kasa gami da bada lambar yabo da aka gudanar a fadar shugaban dake birnin tarayya Abuja

Buhari ya bukaci kungiyar data janye matakin data dauka na yajin aikin, la’akari da halin da daliban Jami’oin kasar ke ciki sakamakon yajin aikin da suka tsunduma.

Ya kuma bukaci kungiyar Dalibai ta kasa NANs ta kara hakuri, kasancewa gwamnati na kokarin shawo kan matsalar.

Buhari yace ko a ranar daya ga watan Fabreru ya umarci shugaban Ma’aikatan Fadar gwamnatin tarayya Farfesa Ibrahim Gambari, Ministan Kwadago da Ayyuka Chris Ngige, da kuma Ministan Ilimi Adamu Adamu, su san mai yiwuwa wajen ganin an magance matsalar yajin aikin

A ranar litinin din wannan makon kungiyar Malaman Jami’ar ta ASUU ta sanar da kara wa’adin yajin aikin da take zuwa watannin Uku (3).

Kungiyar dai na bukatar wasu makudan kudade domin farfado da jami’oin Gwamnati, gami da samar da tsarin biyan albashi na (UTAS) da kuma wasu bukatu da take nema a wajen gwamnatin tarayya Nijeriyar.

Sauran bukatan sun hadar da cika musu alkawarin da gwamantin tarayyar Nijeriyar tayi a cikin wata takardar da aka sanya hannu a alkawarin kungiyar da Gwamantin tarayya na shekarar 2019, tare da nuna rashin gamsuwa da tsarin biyan Albashin bai day ana IPPIS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp