Home General ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 4 A Jihar Benue

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 4 A Jihar Benue

Wani harin ‘Yan Bindiga yayi sanadiyyar halaka akalla mutun 4 a garin Ayilamo dake Karamar Hukumar Logo ta Jihar Benue.

Mazauna garin sun shaidawa PRNigeria cewa lamarin ya auku ne tsakar daren Talata yayin da al’ummar yankin ke tsaka da bacci.

Inda ‘Yan bindigar suka yiwa garin tsinke, tare da tsallakawa gidajen Al’umma inda suka harbe mutum 4 tare da barin wasu cikin muggana raunika.

Guda cikin shuwagabannin al’ummar garin, ya bayyana sunayen wadanda harin ya rutsa dasu da suka hadar da Vaachia Hangeior, Abako Kpeibee, Mtomga Akpi and David Akave.

Kawo lokacin kammala wannan rahoton kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar S.P Catherine Anene bata dauki kiran da muka yi mata ba, kuma bata bada amsar sakon karta kwana da muka tura mata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp