Home Labarai Majalisar Wakilan Nijeriya ta Bukaci Karin Girke Karin Jami’an Tsaro a Jihar...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta Bukaci Karin Girke Karin Jami’an Tsaro a Jihar Taraba

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci Hafsan Sojin kasar da Babban Sifeto Janar su kara girke dakaru a jihar Taraba.

Da yake Karin haske kan kisan da ‘Yan bindiga suka yi a jihar yayin da yake gabatar da kudirin a zaman majalisar na ranar 10 ga watan Mayu, Dan Majalisa daga Jihar Taraba Usman Danjuma yace ‘Yan Bindiga yayin wani hari da ‘Yan Bindigar suka kai tsakar dare sun halaka Al’ummar kauyen da dama.

Mafi yawan Mazauna Kauyen na Tati dai manoma ne, sai dai harin na ‘yan bindiga ya tarwatsasu.

“sakamakon kiraye-kiraye neman dauki da mazauna kauyen suka yi, jami’an tsaro sun yi tattaki zuwa yankin inda ‘yan ta’addan suka yi musu kwantan bauna, inda suka halaka sojoji da shida.

Wannan dai na zuwa ne bayan da ‘yan bindiga suka halaka wani jami’in Dan sanda da wani farar hula a shingen ababen hawa, inda kwamanda bataliya ta 93 yayi batan dabo yayin gudanar da atisayen kawar da ‘Yan Ta’addan.

“an kai korafe-korafe ga jami’an tsaro kan yadda ‘yan bindigar ke zirga-zirga a kauyen a makonnin da suka gabata.

“ wannan ce ta sanya jami’an tsaron Musamman bataliya ta 93 da wasu Karin dakarun hadin gwuiwa, suka farwa ‘yan Ta’addan tare da samun nasarar kwace muggan makamai a hannun su.”

Dan majalisar ya nuna damuwar sa matuka kan yadda ‘yan bindigar ke sake kwarara yankunan Nijeriyar.

Yayin da majalisar ke amincewa da kudirin ta yi kira ga Hukumar Bada Agaji Gaggawata NEMA ta gaggauta kai Agaji ga Al’ummar da abin ya shafa a karamar hukumar Takum ta jihar Taraba.

Da yake ganawa da manema labarai, Danjuma yace ‘yan bindiga sun fito ne daga jihar Borno da jihar Plateau.

“Muna fuskantar babban kalubalen tsaro daga ‘yan bindiga a kudancin jihar Taraba, an kashe sama da mutane 42 cikin kwanaki 3 da suka gabata tare da kone gidaje 6 a karamar hukumar takum, kuma muna zargin ‘yan bindigar sun fito ne daga jihohin Filato da Borno.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp