Home General Rundunar Sojin Najeriya ta Dukufa Wajen Bankado Jami’in Ta da Ya Bata.

Rundunar Sojin Najeriya ta Dukufa Wajen Bankado Jami’in Ta da Ya Bata.

Rundunar Sojin Nijeriya tace ta dukufa wajen bankadowa tare da tseratar da kwamandan sojan da yayi batan dabo yayin gudanar da atisayen kawar da ‘yan ta’adda a jihar Taraba.

Wannan nakunshe ne ta cikin wata takarda mai dauke da sahannun Daraktan yada labaran Rundunar Birgediya Janar Onyema Nwachukwu.

Dakarun dai sun sami kiran waya dake tabbatar da cewa kauyen na Tati na fuskantar harin ‘yan bindiga, sai dai a kokarin sun a fatattakar ‘yan ta’addar suka fada komar su, inda sojoji 6 suka kwanta dama, yayin da babban jami’in soji guda ya bata.

Sai dai Rundunar hadin Gwuiwa ta dakarun sojin da suka kai dauki kauyen Ananum dake karamar hukumar Donga ta jihar, sun hallaka ‘yan bindiga 2 tare da kwato bindiga kirar Ak 47 guda daya, bindiga kirar gida guda daya alburusai masu tsayin 19.7.62mm na musamman baburan hawa guda 3 dai dai sauran muggana makamai.

A halin yanzu dai dakarun sojin na cigaba da bincikar sojojin da suka bata tare da kokarin bankado da maboyar ‘yan ta’addan.

Idan dai za’a iya tunawa Jaridar PRNigeria Hausa ta rawaito cewa dakarun rundunar Sojin bataliya ta 93 sun yi batan dabo, tun bayan suka kai wani sumamen aiki ga maboyar ‘Yan Ta’adda a kauyen Tati dake karamar hukuma Takum ta Jihar Taraba a yammacin Talata.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp