Home Labarai Kungiyar WAMY da Gidauniyar Malam Inuwa Sunyi wa Mutane 2,700 Aikin Ido...

Kungiyar WAMY da Gidauniyar Malam Inuwa Sunyi wa Mutane 2,700 Aikin Ido Kyauta Karo Na Biyu a Jigawa

Kungiyar WAMY da Gidauniyar Malam Inuwa Sunyi wa Mutane 2,700 Aikin Ido Kyauta Karo Na Biyu a Jigawa

 

A daidai lokacin da al’umma da dama ke yawo da jinyoyi kala-kala tare da su saboda yanayin rayuwar yau, ƙungiyar matasa musulmai ta Duniya, World Assembly Of Muslim Youth, (WAMY), da haɗin gwiwar Gidauniyar Malam Inuwa wacce ke ƙarƙashin jagorancin mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, (CCIE), a karo na biyu, sun ɗauki nauyin gudanar da ba da maganin ciwon Ido, raba gilashin ƙara ƙarfin ganin Ido, gami kuma da aikin tiyatar Ido kyauta a Jihar Jigawa domin tallafawa al’umma masu lalurar.

Aikin wanda aka gudanar da shi tsawon kusan mako guda a birnin Dutsen Jihar Jigawa, an yi wa jimillar mutane (636) aikin tiyatar, ya yin da aka ba wa jimillar mutane (600) gilashin ƙara ƙarfin gani, sai kuma jimillar mutum (1,500) waɗanda aka ba wa magungunan ciwon idon.

Bayan kammala aikin a wannan rana, an kuma gudanar da bikin karramawa na musamman ga Likitoci, ma’aikatan lafiya, gami da jami’an tsaro da sauran mutanen da su ka tallafa har aka kai ga samun sa’ar kammaluwar aikin cikin nasara.

Kana kuma, daga bisani gidauniyar ta Malam Inuwa ta shirya liyafa ta musamman domin karrama jami’an gidauniyar ta (WANY), Dakta Isham, da kuma Dakta Bihlali Abdallah, gami da sauran likitocin da su ka tallafa musu a aikin.

A dunƙule, wannan shi ne karo na biyu da aka samu haɗin gwiwa a tsakanin gidauniyar ta (WAMY) da kuma ta Malam Inuwan kan aikin Ido, ba da magani da gilashi kyauta a Jigawa. Hakan kuma shi ne ke zaman karo na uku da gidauniyar ta Malam Inuwa ta samar da irin wannan aikin ido na haɗin gwiwa a Jihar ta Jigawa duba da haɗin gwiwar da ta yi da ƙungiyar ƙasar Qatar da ta haɗakar jami’an lafiya na Duniya aka gudanar da aikin Gumel.

Ɗumbin jama’a da dama sun bayyana godiya da farin cikinsu gami da addu’ar fatan alkhairi. “Waɗanda su ka ɗauki nauyin wannan abu, Allah Ya saka musu da alkhairi, Allah Ya sa su gama lafiya, Allah Ya sa sakamakonsu gidan Aljannah,”. Cewar ɗaya daga cikin waɗanda su ka amfana da aikin, mai suna Alhaji Audu Ali, ɗan asalin yankin Warwaɗe Dam, da ke Dutse.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp