Home General Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta kubutar da Tsoho dan Shekara 75...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta kubutar da Tsoho dan Shekara 75 daga hannun ‘Yan Ta’adda

Rundunar ‘yan sanda jihar zamfara ta sami nasarar kubutar da wani tsoho mai kimanin shekaru 75 daga hannun ‘yan Ta’adda a jihar.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar SP Mohammed Shehu Anipr, a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Kolo Yusuf psc.
Sanarwar tace rundunar a ranar Juma’a ta sami nasarar kubutar da tsohon mai suna Muhammad Shehi dan asalin garin Enagi a karamar hukumar Edati ta jihar Niger, bayan ya kwashe watanni a hannun ‘yan bindigar.
Dakarun rundunar sun gudanar da atisayen ne bayan samun wani rahoton sirri kan sace tsohon, nan suka shiga aiki ba dare ba rana har sai da suka sami nasarar kubutar da shi.
Tsohon ya bayyana wa jami’an cewa wasu gungun ‘yan ta’adda da suka tare hanyar birnin Gwari zuwa Kaduna a farkon watan Oktoban 2022, suka yi awon gaba da su zuwa cikin daji a wani yanki na dan sadau dake jihar ta Zamfara, inda ya kwashe watanni 2 a hannun su.
Sanarwa tace Likitocin sun gudanar da binciken lafiyar sa kafin Jami’an ‘yan sandan su sadashi da iyalen sa.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar ya taya ‘yan uwa da iyalen Muhammad murna bisa samun dan uwan su da suka yi daga bisani ya tabbatar da kudirin hukumar na kare lafiya da dokiyoyin Al’umma

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp