Home DUNIYA Ambaliyar Ruwa ta Hallaka mutane 9 a Afirka ta Kudu

Ambaliyar Ruwa ta Hallaka mutane 9 a Afirka ta Kudu

Mutum tara sun mutu yayin da takwas suka ɓace sakamakon ambaliyar da wani kogi ya yi, inda ya tafi da masu bauta a wani coci.

Shaidu sun ce fiye da masu bauta 30 ne ke tsaye a kan duwatsun da ke kusa da kogin lokacin da ruwan mai gudun gaske ya ratso ta inda suke.

Shaidar ta ƙara da cewa an tsamo Faston da ke jagorantar ibadar bayan da ya maƙale cikin tarin bishiyoyin da ruwan ya taho da su.

Masu aikin ceto da suka haɗar da ‘yan sanda da jami’an kiyaye aukuwar bala’i na ci gaba da nemo waɗanda ruwan ya tafi da su.

Robert Mulaudzi mai magana da yawun ma’aikatar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar ya ce sun samu gawa biyu ranar Asabar, tare da ceto mtum ɗaya wanda ya ce an kai shi asibiti domin kula da lafiyarsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp