Home DUNIYA Ambaliyar Ruwa ta Hallaka mutane 9 a Afirka ta Kudu

Ambaliyar Ruwa ta Hallaka mutane 9 a Afirka ta Kudu

Mutum tara sun mutu yayin da takwas suka ɓace sakamakon ambaliyar da wani kogi ya yi, inda ya tafi da masu bauta a wani coci.

Shaidu sun ce fiye da masu bauta 30 ne ke tsaye a kan duwatsun da ke kusa da kogin lokacin da ruwan mai gudun gaske ya ratso ta inda suke.

Shaidar ta ƙara da cewa an tsamo Faston da ke jagorantar ibadar bayan da ya maƙale cikin tarin bishiyoyin da ruwan ya taho da su.

Masu aikin ceto da suka haɗar da ‘yan sanda da jami’an kiyaye aukuwar bala’i na ci gaba da nemo waɗanda ruwan ya tafi da su.

Robert Mulaudzi mai magana da yawun ma’aikatar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar ya ce sun samu gawa biyu ranar Asabar, tare da ceto mtum ɗaya wanda ya ce an kai shi asibiti domin kula da lafiyarsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp