Home DUNIYA Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bai wa mutanen da ambaliyar Maiduguri ta shafa tallafin dala miliyan shida.

Wata sanarwa da ofishin jami’in kula da ayyukan jin kai a Najeriya, Mohammed Fall ya fitar, ya ce haɗin gwiwar ƙungiyoyin agaji na MDD da masu zaman kansu, ciki har da Red Cross, sun kai ziyara birnin Maiduguri a karshen mako.

A cewarsa, tawagar ta haɗu da mutanen da abin ya shafa – waɗanda yawanci rikicin Boko Haram da kuma rashin tsaro ya riga ya ɗaiɗaita.

“Mu tare da haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi na samar wa da mutanen kayan abinci, muna kuma jefa musu abinci ta sama a wuraren da ke wahalar kai wa, har ma da ruwan sha,” in ji shi

Ya kuma ce suna kula da lafiyar waɗanda aka tsugunar a sansanoni musamman ma mata da yara mata da kuma tabbatar da cewa ba a samu ɓarkewar cutuka ba.

Ambaliyar ta afku ne bayan fashewar madatsar ruwa ta Alau wanda ke nisan kilomita goma da kudancin Maiduguri.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp