Home DUNIYA Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bai wa mutanen da ambaliyar Maiduguri ta shafa tallafin dala miliyan shida.

Wata sanarwa da ofishin jami’in kula da ayyukan jin kai a Najeriya, Mohammed Fall ya fitar, ya ce haɗin gwiwar ƙungiyoyin agaji na MDD da masu zaman kansu, ciki har da Red Cross, sun kai ziyara birnin Maiduguri a karshen mako.

A cewarsa, tawagar ta haɗu da mutanen da abin ya shafa – waɗanda yawanci rikicin Boko Haram da kuma rashin tsaro ya riga ya ɗaiɗaita.

“Mu tare da haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi na samar wa da mutanen kayan abinci, muna kuma jefa musu abinci ta sama a wuraren da ke wahalar kai wa, har ma da ruwan sha,” in ji shi

Ya kuma ce suna kula da lafiyar waɗanda aka tsugunar a sansanoni musamman ma mata da yara mata da kuma tabbatar da cewa ba a samu ɓarkewar cutuka ba.

Ambaliyar ta afku ne bayan fashewar madatsar ruwa ta Alau wanda ke nisan kilomita goma da kudancin Maiduguri.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp