Home DUNIYA Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bai wa mutanen da ambaliyar Maiduguri ta shafa tallafin dala miliyan shida.

Wata sanarwa da ofishin jami’in kula da ayyukan jin kai a Najeriya, Mohammed Fall ya fitar, ya ce haɗin gwiwar ƙungiyoyin agaji na MDD da masu zaman kansu, ciki har da Red Cross, sun kai ziyara birnin Maiduguri a karshen mako.

A cewarsa, tawagar ta haɗu da mutanen da abin ya shafa – waɗanda yawanci rikicin Boko Haram da kuma rashin tsaro ya riga ya ɗaiɗaita.

“Mu tare da haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi na samar wa da mutanen kayan abinci, muna kuma jefa musu abinci ta sama a wuraren da ke wahalar kai wa, har ma da ruwan sha,” in ji shi

Ya kuma ce suna kula da lafiyar waɗanda aka tsugunar a sansanoni musamman ma mata da yara mata da kuma tabbatar da cewa ba a samu ɓarkewar cutuka ba.

Ambaliyar ta afku ne bayan fashewar madatsar ruwa ta Alau wanda ke nisan kilomita goma da kudancin Maiduguri.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp