Home DUNIYA Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

Food

Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

 

Hauhawar farashi a Najeriya ya ƙaru sosai a watan Maris a karon farko cikin wannan shekara, kamar yadda alƙaluma daga hukumar ƙididiga ta ƙasar suka nuna.

Ana ganin lamarin zai ƙara haifar da cikas ga gwamnatin ƙasar ƙarƙashin Bola Ahmed Tinubu a daidai lokacin da ake tunkarar zaɓukan 2027 a watan Junairun baɗi.

Ƙasar wadda ta fi kowace ƙasa yawan al’umma a Afrika na ta ƙokarin rage hauhawar farashi kafin a fara yaƙin Iran, inda gwamnatin ke ta ɗaukar matakai da dama a cikin watanni 11 da suka gabata.

Sai dai yaƙin Gabas ta Tsakiya ya mayar da hannun agogo baya musamman sakamakon tashin farashin man fetur, inda ya shafi farashin kayan masarufi.

Hukumar NBS a ƙasar ta ce hauhawar farashi ta ƙaru daga 15.06% a watan Fabrairu zuwa 15.38% a watan Maris.

Hauhawar farashin kayan abinci kuma ta ƙaru daga 12.12% zuwa 14.31%

Wasu al’ummar ƙasar sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa hauhawar farashin da ake samu a Najeriya na ƙara jefa rayuwarsu cikin matsi da ƙunci.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Raphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - AtikuCOAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a Edo
X whatsapp