Home DUNIYA Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

Food

Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

 

Hauhawar farashi a Najeriya ya ƙaru sosai a watan Maris a karon farko cikin wannan shekara, kamar yadda alƙaluma daga hukumar ƙididiga ta ƙasar suka nuna.

Ana ganin lamarin zai ƙara haifar da cikas ga gwamnatin ƙasar ƙarƙashin Bola Ahmed Tinubu a daidai lokacin da ake tunkarar zaɓukan 2027 a watan Junairun baɗi.

Ƙasar wadda ta fi kowace ƙasa yawan al’umma a Afrika na ta ƙokarin rage hauhawar farashi kafin a fara yaƙin Iran, inda gwamnatin ke ta ɗaukar matakai da dama a cikin watanni 11 da suka gabata.

Sai dai yaƙin Gabas ta Tsakiya ya mayar da hannun agogo baya musamman sakamakon tashin farashin man fetur, inda ya shafi farashin kayan masarufi.

Hukumar NBS a ƙasar ta ce hauhawar farashi ta ƙaru daga 15.06% a watan Fabrairu zuwa 15.38% a watan Maris.

Hauhawar farashin kayan abinci kuma ta ƙaru daga 12.12% zuwa 14.31%

Wasu al’ummar ƙasar sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa hauhawar farashin da ake samu a Najeriya na ƙara jefa rayuwarsu cikin matsi da ƙunci.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp