Home DUNIYA Fursunoni 63 sun gurfana gaban kotun Sojin Congo kan laifukan kisa da...

Fursunoni 63 sun gurfana gaban kotun Sojin Congo kan laifukan kisa da fyaɗe

Akalla fursuna 63 sun gurfana a gaban wata kotun Soji da ke tsakiya birnin Kinshasa na Jamhuriya Dimokradiyar Congo a jiya laraba inda za su fuskanci tuhuma kan zarginsu da hanu a kisan mutane 130 da kuma aikata fyade.

Wadanda ake zargin sun bayyana ne a gaban wata kotun sojoji da ke a harabar gidan kason Makala a babban birnin ƙasar Kinshasa.

Lauyoyin fursunonin sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa ana tuhumar mutanen da suke karewa da laifukan lalata gine gine da haddasa gobara da kuma ayyukan ta’addanci baya ga aikata fyade.

A zaman da ta yi na farko a makon jiya an fuskanci rashin fahimtar juna dangane da laifuka da ake zargin mutanen da aikatawa.

A cikin daren 1 wayewar 2 ga watan satumban nan fursunoni da dama sukayi yunkurin tserewa daga gidan kaso ba tare da yin karin haske game da irin yanayin da lamarin ya afku ba.

Alkalumman wucin gadi da gwamnati ta fitar na cewa akalla mutum 129 suka mutu, 24 daga ciki an harbe su ne da bindiga, gabanin washegari mahukuntan kasar su fitar ƙarin adadin mutun biyu da suka mutu sakamakon raunukan da suka ji.

Ƙungiyar Tarayya Turai, da offishoshin jakadancin Faransa da Belguim dukanin su sun bukaci yin haske game da lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp