Home DUNIYA Mali ta sake dakatar da kafar talabijin mallakin Faransa TV5 Monde

Mali ta sake dakatar da kafar talabijin mallakin Faransa TV5 Monde

Gwamnatin Sojin Mali ta dakatar da yaɗa shirye-shiryen gidan talabijin na TV5 a ƙasar har na tsawon watanni 3 bayan zargin tashar da yaɗa labaran rashin adalci a shirye-shiryenta sakamakon fitar da bayanai ba tare da jin dukkanin ɓangarorin da labarin ya shafa ba.

Tashar ta TV5 mai yaɗa shirye-shiryenta da harshen faransanci ita da kanta da sanar da wannan hukunci na mahukuntan na Mali ga kamfanin dillancin labarai na AFP.

Sanarwar da Sojin na Mali suka fitar sun ce hukuncin zai fara aiki nan ta ke wato daga jiya 11 ga watan Stumban da muke ciki.

Hukumomin na sojin na Mali sun zargin wannan tashar da bada labarai da suka sabawa dokokin ƙasar.

Da samun wannan labari, kungiyoyi kare hakokin ƴan jarida ta kasa da kasa wato RSF da babbar murya ta na mai bayyana damuwa da kuma takaici ganin ta yada hukumomin sojin Mali suka aiwatar da wannan mataki ba tare da tuntuba ba.

Matakin shi ne na dakatar da watsa shirye-shiryen wannan tasha na tsawon watanni uku bisa zargin su da rashin daidaito a fannin yada labarai biyo bayan farmaki dakarun kasar a yankin Tinzaoutaene.

Hukumar Kula da Sadarwa ta kasar ta Mali (HAC) ta soki tashar ta TV5 Monde da bayar da rahoto a ranar 25 ga Agusta, a cikin labarun ta na Afirka, mutuwar akalla fararen hula goma sha biyar a harin da jirage marasa matuka a Tinzaouatène da ke arewacin kasar ta Mali.

Tashar ta TV5  a cikin wata sanarwa ta na mai nadama da kuma nuna mamakin ta na ganin hukumar kula da sadarwa ta kasar ta Mali ba ta nemi jin ko ta bakin masu wakiltar wannan tashar ba kafin daukar irin wannan mataki .

Ko a ƴan shekarun da suka gabata, ƴan lokuta bayan juyin mulkin sojojin kasar an dakatar da kafofin watsa labarai da yawa da kafafan yada labarai na France24 da kuma Radio France Internationale (RFI).

Haka zalika Sojin na Mali sun kuma dakatar da France2 a farkon shekarar 2024, kafin LCI ta fuskanci irin wannan makoma a karshen watan Agusta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp