Home DUNIYA EU da Jamus sun bai wa Najeriya tallafin kusan yuro miliyan 18

EU da Jamus sun bai wa Najeriya tallafin kusan yuro miliyan 18

Kungiyar tarayyar turai da ƙasar Jamus sun ƙaddamar da kaso na 3 na shirin tallafawa Najeriya dangane da abinda ya shafi makamashi NESP domin habbaka sabbin hanyoyin samar da isashshen makamashi musamman a yankunan karkara.

Shirin zai laƙume kuɗin da ya kusa yuro miliyan 18 inda za a sada mutane 1,500 da lantarki da kuma samarwa da mutane dubu 30 gas na girki.

Har wa yau a kashi na 3 na wannan shirin za a samar da wutar lantarki mai ƙarfin Megawatts 8.

Tallafin na samar da makamashi ga Najeriya an fara ƙaddamar da shi tun a shekarar 2013 wanda kungiyar tarayyar turai EU da tallafin ƙasar Jamus haɗin gwiwa da ma’aikatar lantarki ta Najeiya.

Kungiyar ta tarayyar turai ta amince ta ƙara zuba kuɗi a kashi na 3 na wannan shiri domin taimakawa ci gaban da kuma samar da tsarin lantarki ta sabbin hanyoyin makamashi da kuma tabbatar da jama’a sun amafana da shirin.

Mataimakin Ambasadan ƙasar Jamus Johannes Lenhre ya tabbatar da shiri ƙasarsa wurin cimma muradan da Najeriya ta snaya a gaba a fannin makamashi.

Sakataran ma’aikatar lantarki a Najeriya Mahmuda Mamman ya yaba da irin tallafin da Najeriya ke samu daga kungiyar tarayyar turai da Jamus musamman yadda suke ƙoƙarin tabbatar da samun isashshen makamashi a ƙasar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp