Home AFIRKA An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

Wannan ya biyo bayan hukuncin kotu da ya bada damar rantsar da sabon mataimakin biyo bayan tsige tsohon mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua a watan da ya gabata.

Babbar kotu a Kenya ce ta dakatar da rantsar da Kindiki bayan Gachagua da magoya bayansa sun shigar da ƙarar ƙalubalantar tsigeshi da majalisun dokokin ƙasar biyu suka yi.

To sai dai  a ranar Alhamis kotu ta janye dakatarwar da aka yi na rantsar da Rigathi Gachagua a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya.

Kotun ƙoli a Kenya ce ta bayar da umarnin rantsar da sabon mataimakin shugaban ƙasa, bayan majalisun dokokin ƙasar biyu suka tsige Rigathi Gachagua daga muƙaminsa.

An dai share tsawon watanni ana fama da rikici tsakanin Shugaba William Ruto da mataimakinsa Rigathi Gachagua, to sai dai a ranar 17 ga watan oktoban da ya gabata rikicin ya ɗauki sabon salo inda har ta kai ƙarama da kuma babbar majalisar dokokin dokokin ƙasar suka kaɗa ƙuri’ar kawo ƙarshen mulkinsa.

Wanda ake shirin rantsarwa a wannan juma’a wato ministan cikin gida Kithure Kindiki, mutum ne mai shekaru 52 a duniya, kuma ya yi fice saboda kasancewarsa kasaitaccen malamin jami’a, kafin daga bisani ya tsunduma siyasa daga-gadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp