Home AFIRKA An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

Wannan ya biyo bayan hukuncin kotu da ya bada damar rantsar da sabon mataimakin biyo bayan tsige tsohon mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua a watan da ya gabata.

Babbar kotu a Kenya ce ta dakatar da rantsar da Kindiki bayan Gachagua da magoya bayansa sun shigar da ƙarar ƙalubalantar tsigeshi da majalisun dokokin ƙasar biyu suka yi.

To sai dai  a ranar Alhamis kotu ta janye dakatarwar da aka yi na rantsar da Rigathi Gachagua a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya.

Kotun ƙoli a Kenya ce ta bayar da umarnin rantsar da sabon mataimakin shugaban ƙasa, bayan majalisun dokokin ƙasar biyu suka tsige Rigathi Gachagua daga muƙaminsa.

An dai share tsawon watanni ana fama da rikici tsakanin Shugaba William Ruto da mataimakinsa Rigathi Gachagua, to sai dai a ranar 17 ga watan oktoban da ya gabata rikicin ya ɗauki sabon salo inda har ta kai ƙarama da kuma babbar majalisar dokokin dokokin ƙasar suka kaɗa ƙuri’ar kawo ƙarshen mulkinsa.

Wanda ake shirin rantsarwa a wannan juma’a wato ministan cikin gida Kithure Kindiki, mutum ne mai shekaru 52 a duniya, kuma ya yi fice saboda kasancewarsa kasaitaccen malamin jami’a, kafin daga bisani ya tsunduma siyasa daga-gadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp