Home AFIRKA Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera

Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera


Madugun adawa na jamhuriyyar Afrika ta tsakiya, Anicet-George Dologuele yayi watsi da sakamakon zaɓen ƙasar da ke bayyana shugaba Faustin-Archange Touadera a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen watan jiya.

Tun gabanin sakamako Touadera mai shekaru 68 shi ne aka yiwa tsammanin ya lashe zaɓen yayinda sakamako ya nuna shi a matsayin wanda ya samu fiye da kashi 76 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa.

Nasarar kai tsaye ta baiwa Touadera damar ci gaba da mulki a wa’adi na 3, bayan da tun a watan Oktoban bara ya sanar da aniyar sake tsayawa takara lamarin da ƴan adawa ke yiwa kallo a matsayin wani yunƙurin ci gaba da mulkin kama karya a ƙasar.

Sai dai madugun adawar Dologuele wanda ya samu kashi 15 na yawan ƙuri’un da aka ƙada a zaɓen da ya bashi damar zuwa na biyu ya ce an tafka maguɗi ne a zaɓen tare da sauya sakamako.

A cewar Dologuele ba a baiwa jama’a sakamakon abin da suka zaɓa ba, ta yadda hukumar zaɓe ta yi zuraren ƙuri’u a wasu wuraren don nuna shugaban a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Shugaba Faustin-Archange Touadera wanda ke samun cikakken goyon bayan Rasha da ta tallafa masa wajen kawo ƙarshen yaƙin da ƙasar ke fuskanta kai tsaye nasarar ta bashi damar ci gaba da jan ragamar ƙasa har zuwa ƙarin shekaru 5 a wa’adi na 3.

Ana kallon nasarar da ya yi ta kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe a jamhuriyyar Afrikan ta tsakiya ya taimaka masa matuƙa wajen samun cikakken goyon bayan jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp