Home AFIRKA Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera

Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera


Madugun adawa na jamhuriyyar Afrika ta tsakiya, Anicet-George Dologuele yayi watsi da sakamakon zaɓen ƙasar da ke bayyana shugaba Faustin-Archange Touadera a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen watan jiya.

Tun gabanin sakamako Touadera mai shekaru 68 shi ne aka yiwa tsammanin ya lashe zaɓen yayinda sakamako ya nuna shi a matsayin wanda ya samu fiye da kashi 76 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa.

Nasarar kai tsaye ta baiwa Touadera damar ci gaba da mulki a wa’adi na 3, bayan da tun a watan Oktoban bara ya sanar da aniyar sake tsayawa takara lamarin da ƴan adawa ke yiwa kallo a matsayin wani yunƙurin ci gaba da mulkin kama karya a ƙasar.

Sai dai madugun adawar Dologuele wanda ya samu kashi 15 na yawan ƙuri’un da aka ƙada a zaɓen da ya bashi damar zuwa na biyu ya ce an tafka maguɗi ne a zaɓen tare da sauya sakamako.

A cewar Dologuele ba a baiwa jama’a sakamakon abin da suka zaɓa ba, ta yadda hukumar zaɓe ta yi zuraren ƙuri’u a wasu wuraren don nuna shugaban a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Shugaba Faustin-Archange Touadera wanda ke samun cikakken goyon bayan Rasha da ta tallafa masa wajen kawo ƙarshen yaƙin da ƙasar ke fuskanta kai tsaye nasarar ta bashi damar ci gaba da jan ragamar ƙasa har zuwa ƙarin shekaru 5 a wa’adi na 3.

Ana kallon nasarar da ya yi ta kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe a jamhuriyyar Afrikan ta tsakiya ya taimaka masa matuƙa wajen samun cikakken goyon bayan jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp