Home Labarai APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara

APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara

Jam’iyyar APC reshen jihar Rivers ta yi fatali da yunƙurin tsige gwamnan jihar, Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar ke shirin yi.

Cikin wata sanarwa da APC ta fitar ta ce duk da cewa tana girmama cin gashin kan majalaisar dokoki, amma ba za ta amince da yunƙurin tsige gwamnan ba.

A ranar Alhamis ne majalisar dokokin jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya ta ƙaddamar da yunƙurin sake tsige gwamnan da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, saboda zarginsu da laifukan da suka saɓa ƙa’idar aiki.

Jam’iyyar APC da ke mulkin jihar ta bayyana shirin da yunƙurin ”tayar da hargisti” a jihar.

APC ta kuma yi kira ga mambobin majalisar dokokin jihar su kauce wa duk wani yunƙuri da zai jefa jihar cikin rikicin siyasa.

A watan da ya gabata ne dai Gwamna Fubara ya koma APC bayan ficewarsa daga PDP.

Tun bayan zaɓen 2023, jihar – mai arzikin man fetur – ta faɗa rikicin siyasa sakamakon saɓanin da gwamnan jihar Siminalayi Fubara ya samu da ministan Abuja, wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Nysome Wike.

Ricikin ya ci gaba da ƙamari, lamarin da ya kai ga shugaban ƙasar, Bola Tinubu ayyana dokar ta-ɓaci a jihar tare da dakatar da Gwamnan Fubara har na tsawon wata shida a shekarar da ta gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp