Home Labarai APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara

APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara

Jam’iyyar APC reshen jihar Rivers ta yi fatali da yunƙurin tsige gwamnan jihar, Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar ke shirin yi.

Cikin wata sanarwa da APC ta fitar ta ce duk da cewa tana girmama cin gashin kan majalaisar dokoki, amma ba za ta amince da yunƙurin tsige gwamnan ba.

A ranar Alhamis ne majalisar dokokin jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya ta ƙaddamar da yunƙurin sake tsige gwamnan da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, saboda zarginsu da laifukan da suka saɓa ƙa’idar aiki.

Jam’iyyar APC da ke mulkin jihar ta bayyana shirin da yunƙurin ”tayar da hargisti” a jihar.

APC ta kuma yi kira ga mambobin majalisar dokokin jihar su kauce wa duk wani yunƙuri da zai jefa jihar cikin rikicin siyasa.

A watan da ya gabata ne dai Gwamna Fubara ya koma APC bayan ficewarsa daga PDP.

Tun bayan zaɓen 2023, jihar – mai arzikin man fetur – ta faɗa rikicin siyasa sakamakon saɓanin da gwamnan jihar Siminalayi Fubara ya samu da ministan Abuja, wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Nysome Wike.

Ricikin ya ci gaba da ƙamari, lamarin da ya kai ga shugaban ƙasar, Bola Tinubu ayyana dokar ta-ɓaci a jihar tare da dakatar da Gwamnan Fubara har na tsawon wata shida a shekarar da ta gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp