Home Labarai Dangote ya kai ƙarar tsohon shugaban NMDPRA zuwa EFCC

Dangote ya kai ƙarar tsohon shugaban NMDPRA zuwa EFCC

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya kai ƙarar tsohon shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da kuma sufurin man fetur ta Najeriya, NMDPR, Farouk Ahmed, gaban EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa.

Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ruwaito wata sanarwa daga kamfanin Dangoten, cewa shugaban kamfanin ya shigar da ƙarar Farouk a shalkwatar hukumar ta EFCC.

A baya Dangote ya shigar da ƙarar Forouk gaban hukumar ICPC mai yaƙi da almundahana a Najeriya, domin bincikarsa kan zargin kashe dala miliyan biyar wajen karatun sakandiren ƴaƴansa a ƙasar Switzerland.

Wani abu da ake ganin ya sa Shugaban ƙasar Bola Tinubu sauke shi daga muƙamain nasa.

Sai dai a kwanakin da suka gabata ne Dangote ya janye ƙorafin nasa daga hukumar ICPC, kodayake hukumar ta ce za ta ci gaba da binciken nata.

Sanarwar Dangoten ta ce ta janye ƙorafin daga ICPC ne domin samun damar shigar da sabon ƙorafi gaban hukumar EFCC.

A ƙorafin nasa Dangote ya buƙaci EFCC ta binciki Farouk bisa zargin tafka almundana da amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba, tare da gurfanar da shi a gaban kotu idan aka same shi da laifi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp