Home AFIRKA yadda mahara suka hallaka sojojin Nijar sama da 30

yadda mahara suka hallaka sojojin Nijar sama da 30

Aƙalla sojoji 34 ne wasu mahara da ake zargin masu ikirarin jihadi sun kashe a Jamhuriyar Nijar, sannan suka jikkata wasu mutum 14.

An kai harin ne a garin Banibangou, wanda ke kan iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso, inda ake tunanin akwai mahara masu ikirarin jihadi da suke da alaƙa da ƙungiyar Al Qaeda.

Ma’aikatar tsaron Nijar ta yi Allah-wadai da harin, wanda ta bayyana da “na rashin hankali,”.

Ma’aikatar ta ce “an kai harin ne a ranar Alhamis 19 ga watan Yuni. Wanda hari ne na dabbanci da aka kai a garin Banibangou, wanda wasu mahara waɗanda baƙi ne suka kai a babura sama 200,” kamar yadda ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin ƙasar sun kashe “gomman maharan,” a lokacin da suke musayar wuta, sannan ta tura ƙarin jami’a zuwa yankin.

A yanzu haka dai Nijar da Burkina Faso da Mali suna ƙarƙashin mulkin soji ne waɗanda suka ƙwace mulki bayan hamɓarar da zaɓaɓɓun shugabannin ƙasar, sannan suka kafa ƙawancen tsaro.

Sai dai duk da ƙawancen, har yanzu ƙasashen yankin suna fama da rikice-rikice a ƴan watannin da ake ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp