Home AFIRKA yadda mahara suka hallaka sojojin Nijar sama da 30

yadda mahara suka hallaka sojojin Nijar sama da 30

Aƙalla sojoji 34 ne wasu mahara da ake zargin masu ikirarin jihadi sun kashe a Jamhuriyar Nijar, sannan suka jikkata wasu mutum 14.

An kai harin ne a garin Banibangou, wanda ke kan iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso, inda ake tunanin akwai mahara masu ikirarin jihadi da suke da alaƙa da ƙungiyar Al Qaeda.

Ma’aikatar tsaron Nijar ta yi Allah-wadai da harin, wanda ta bayyana da “na rashin hankali,”.

Ma’aikatar ta ce “an kai harin ne a ranar Alhamis 19 ga watan Yuni. Wanda hari ne na dabbanci da aka kai a garin Banibangou, wanda wasu mahara waɗanda baƙi ne suka kai a babura sama 200,” kamar yadda ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin ƙasar sun kashe “gomman maharan,” a lokacin da suke musayar wuta, sannan ta tura ƙarin jami’a zuwa yankin.

A yanzu haka dai Nijar da Burkina Faso da Mali suna ƙarƙashin mulkin soji ne waɗanda suka ƙwace mulki bayan hamɓarar da zaɓaɓɓun shugabannin ƙasar, sannan suka kafa ƙawancen tsaro.

Sai dai duk da ƙawancen, har yanzu ƙasashen yankin suna fama da rikice-rikice a ƴan watannin da ake ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp