Home General Mutane 5 sun gamu da ajalinsu sakamakon fashewar wani abu a Kano

Mutane 5 sun gamu da ajalinsu sakamakon fashewar wani abu a Kano

Aƙalla mutane biyar aka tabbatar  sun mutu, kana wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani abu da ake zargin bam ne a Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Rundunar ƴansandan jihar, ta bakin kwamishinanta, Ibrahim Adamu Bakori, wadda ta tabbatar da aukuwar lamarin, ta ce ya faru ne akan bypass na Mariri dake yammacin birnin Kano.

Rahotanni sun ce jami’an ƴansanda da na hukumar agajin gaggawa sun garzayar wurin da aka samu fashewar domin kai ɗauki, a yayin da lamarin ya haddasa ruɗani da firgici a zukatan al’ummar yankin.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke jigilarsa ne wanda aka yi sakaci ya fashe.

Binciken farko-farko ya nuna cewa abin fashewar na cikin wata babbar mota ce, wadda ta ɗauko kaya, mallakain wasu masu sana’ar gwangwan, kuma take kan hanyar zuwa Jihar Yobe.

Rundunar ƴansandan Kanon ta ce ta gani wasu ƙakkrin abubuwan fashewa da ba su kai ga tashi ba a inda lamarin ya faru, kuma  tana  cigaba da bincike akan yadda aka samo su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp