Home General An yi Jana’izar mutum 10 da ƴar kumar bakin wake ta hallaka...

An yi Jana’izar mutum 10 da ƴar kumar bakin wake ta hallaka a Borno

Rundunar ƴansandan jihar ta tabbatar da harin da wata ƴar ƙunar bakin wake ta kai a babbar kasuwar kifi da ke Konduga, inda ta ce aƙalla mutum 10 sun mutu, duk da wata majiya ta ce aƙalla mutum 20 ne suka mutu, ciki har da ƴan sa-kai da suke taimakon sojoji wajen yaƙin da ƴan ƙungiyar.

A daren Juma’a na 20 ga Yuni, 2025 ne rahotani suka nuna cewa wata ƴar ƙunar bakin waken ta kai harin a garin na Konduga, wanda ke kusa da Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Da yake magana game da harin, mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya yi Allah wadai da harin, sannan ya yi kira ga jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

An ga wasu hotuna da aka jera gawarwakin waɗanda harin ya rutsa da su a lokacin da ake shirin yi musu jana’iza.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp