Home General Wani kamfani zai fara samar da kayan gwajin cutar HIV da kuma...

Wani kamfani zai fara samar da kayan gwajin cutar HIV da kuma Malaria a Najeriya

Wani kamfanin samar da magunguna a Najeriya Codix Bio, na shirin samar da kayayykin gwajin cuta mai karya garkuwar jiki da kuma Malaria, biyo bayan matakin Amurka na janye bada tallafin irin waɗannan kayayaki da ake bayarwa.

Amurka ce ƙasar da ta fi kowacce bai wa hukumomin lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya talafi, saboda haka ƙasashe masu tasowa ke kan hanyar tagayyara matukar ba a sami wata hanyar samar da kayayyskin lafiyar ba.

Wannan lamari dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ƙasar ke ƙoƙari, wajen kawo ƙarshen cutar zazzaɓin cizon sauro da kuma rage yawan masu kamuwa da cuta mai karya garkuwar jiki.

Bayanai sun ce kamfanin na da ƙarfin da zai iya samar da kayayykin gwajin guda miliyan 147 duk shekara, amma sannun a hankali zai iya kaiwa miliyan 160.

A cewar shugaban kamfanin Olanrewaju Balaja, matukar aikin ya sami nasarar da ake bukata, kamfanin zai faɗaɗa ayyukan sa zuwa sauran sassan Africa, musamman ƙasashen kudu da hamada.

Kawo yanzu dai babu bayani ƙarara kan yadda Najeriya za ta ji jiki da matakin na Amurka, amma mahukunta sun ce sun kara yawan kuɗaɗen da suke warewa ɓangaren lafiya don cike gibin janye tallafin da Amurka ta yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp