Home General Wani kamfani zai fara samar da kayan gwajin cutar HIV da kuma...

Wani kamfani zai fara samar da kayan gwajin cutar HIV da kuma Malaria a Najeriya

Wani kamfanin samar da magunguna a Najeriya Codix Bio, na shirin samar da kayayykin gwajin cuta mai karya garkuwar jiki da kuma Malaria, biyo bayan matakin Amurka na janye bada tallafin irin waɗannan kayayaki da ake bayarwa.

Amurka ce ƙasar da ta fi kowacce bai wa hukumomin lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya talafi, saboda haka ƙasashe masu tasowa ke kan hanyar tagayyara matukar ba a sami wata hanyar samar da kayayyskin lafiyar ba.

Wannan lamari dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ƙasar ke ƙoƙari, wajen kawo ƙarshen cutar zazzaɓin cizon sauro da kuma rage yawan masu kamuwa da cuta mai karya garkuwar jiki.

Bayanai sun ce kamfanin na da ƙarfin da zai iya samar da kayayykin gwajin guda miliyan 147 duk shekara, amma sannun a hankali zai iya kaiwa miliyan 160.

A cewar shugaban kamfanin Olanrewaju Balaja, matukar aikin ya sami nasarar da ake bukata, kamfanin zai faɗaɗa ayyukan sa zuwa sauran sassan Africa, musamman ƙasashen kudu da hamada.

Kawo yanzu dai babu bayani ƙarara kan yadda Najeriya za ta ji jiki da matakin na Amurka, amma mahukunta sun ce sun kara yawan kuɗaɗen da suke warewa ɓangaren lafiya don cike gibin janye tallafin da Amurka ta yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp