Home General Sojojin Najeriya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP

Sojojin Najeriya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP

Nigerian Army

Rundunar sojojin Najeriya ta samu gagarumar nasarar kashe manyan manyan kwamandojin Boko Haram da na tsagin ISWAP, a wasu hare-hare da ta kai a makon da ya gabata da kuma wannan makon da mu ke ciki.

A wasu hare-hare da sojojin da ke aiki a ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai suka kai garuruwan Mallam Fatori da kuma Buratai na jihar Borno a makon da ya gabata, sun samu nasarar kashe kwamandojin Boko Haram uku da suka haɗa da Amir Abu Ali da Amir Ibunu sai kuma Amir Abu Waldume.

Haka nan a wani harin na daban da suka kai Nzalgana na jihar Yobe da kuma Timbuktu na jihar Borno, jami’an tsaron na Najeriya sun kashe Ameer Malam Jidda, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin Boko Haram a garin Ngorgore da Malumti.

Kisan manyan jagororin Boko Haram da sojojin Najeriya suka dai ya raunata tsarin shugabancinsu da kuma sanyasu cikin ɗimuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp