Home AFIRKA Nijeriya ta sake ciwo bashi don samar da Lantarki

Nijeriya ta sake ciwo bashi don samar da Lantarki

Najeriya ta karɓo rancen dala biliyan 1.1 daga bankin raya Afirka (AfDB) don samar da wutar lantarki ga mutane miliyan 5 daga yanzu zuwa ƙarshen shekarar 2026.

A cewar Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman, Shugaba Bola Tinubu ya bayyana hakan a cikin jawabin da Adebayo Adelabu, ministan wutar lantarki, ya gabatar, a taron da aka kammala na kwanaki biyu na inganta ɓangaren makamashi na Afirka a Dar es. Salaam, babban birnin ƙasar Tanzania.

Tinubu ya kuma bayyana cewa za a yi amfani da dala miliyan 200 na AfDB domin samar da wutar lantarki ga mutane 500,000 a ƙarshen shekarar 2025.

“Wannan babban buri ne, amma za mu iya cimma shi tare,” in ji Tinubu.

“A matsayina na shugaban Najeriya, na himmatu wajen ba aiwatar da aikin samar da makamashi, kuma mun ba da babban fifiko.”

Ya ƙara da cewa “Kamar yadda muka sani, Afirka na da wadatar albarkatun makamashi, amma har yanzu miliyoyin ƴan nahiyar mu ba sa samun ingantaccen makamashi mai araha.”

Shugaba Tinubu kuma jinjinawa Ajay Banga, shugaban bankin duniya, da Akinwunmi Adesina na AfDB saboda hangen nesan su na kawo sauyi, wanda ya ce “zai haskaka da kuma karfafa Afirka.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp