Home AFIRKA ECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a...

ECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a hukumance

Kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen Yammacin Afirka ta ECOWAS ta tabbatar da ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da kuma Nijar a hukumance

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da ECOWAS din ta fitar, tana mai cewa har yanzu kofa a bude take ga wadannan kasashe, a duk lokacin da suka sauya shawarar sake koma wa.

A cikin sanarwar, ECOWAS ta ce za a ci gaba da mutunta fasfon jama’ar wadannan kasashe uku da ke dauke da tambarin ECOWAS, hadi da katinsu na shaidar dan kasa.

Haka zalika kungiyar ta ce za a ci gaba da kallon wadannan kasashe tamkar mambobinta, har ma ta bayyana a cikin sanarwar cewa, harkokin kasuwanci tsakanin kasashe mambobin ECOWAS da kuma kasashen Nijar, Burkina Faso da kuma Mali zasu ci gaba da tafiya kamar yadda suke a baya.

Sanarwar ta kuma bukaci kasashen kungiyar, da su ci gaba da bawa jama’ar kasashen uku damar shiga kasashensu ba tare da takardar izinin shiga ba, da kuma zama, har sai baba ta gani.

Kungiyar ta ce an fitar da wannan sanarwa ne, domin kaucewa haifar da zaman tankiya ko kuma dardar tsakanin jama’ar wadannan kasashe uku, musamman ‘yan kasuwa, da kuma kwantar musu da hankula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp