Home AFIRKA ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

Ƙungiyar ECOWAS ta dakatar da Guinea-Bissau kwanaki biyu bayan juyin mulkin da ya kawo ƙarshen gwamnatin shugaba Umaro Sissoco Embalo daidai lokacin da ake dakon sakamakon zaɓen da shugaban ke neman tazarce.

ECOWAS ta bayyana juyin mulkin na Guinea Bissau a matsayin babbar barazana ga tsarin dimokaraɗiyya a ƙasar ta yammacin Afrika.

Cikin matsayar da wannan taro na ECOWAS ya cimma, akwai dakatar da wannan ƙungiyar da kuma matsa mata lamba don ganin ta koma mulkin farar hula don tabbatar da demokraɗiyya.

Tuni dai hamɓararren shugaban na Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embalo ya sauka a ƙasar Senegal a wani jirgi na musamman jiya Alhamis, biyo bayan shiga tsakani da ƙungiyar ECOWAS ta yi, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Senegal ta bayyana.

Wannan ne juyin mulki na 9 da ake fuskanta a ƙasashen yammaci da Tsakiyar Afirka cikin shekaru biyar da suka gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp