Home AFIRKA ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

Ƙungiyar ECOWAS ta dakatar da Guinea-Bissau kwanaki biyu bayan juyin mulkin da ya kawo ƙarshen gwamnatin shugaba Umaro Sissoco Embalo daidai lokacin da ake dakon sakamakon zaɓen da shugaban ke neman tazarce.

ECOWAS ta bayyana juyin mulkin na Guinea Bissau a matsayin babbar barazana ga tsarin dimokaraɗiyya a ƙasar ta yammacin Afrika.

Cikin matsayar da wannan taro na ECOWAS ya cimma, akwai dakatar da wannan ƙungiyar da kuma matsa mata lamba don ganin ta koma mulkin farar hula don tabbatar da demokraɗiyya.

Tuni dai hamɓararren shugaban na Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embalo ya sauka a ƙasar Senegal a wani jirgi na musamman jiya Alhamis, biyo bayan shiga tsakani da ƙungiyar ECOWAS ta yi, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Senegal ta bayyana.

Wannan ne juyin mulki na 9 da ake fuskanta a ƙasashen yammaci da Tsakiyar Afirka cikin shekaru biyar da suka gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp