Home AFIRKA Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a...

Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a Nijar

Aƙalla tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 ne mahukunta Jamhuriyyar Nijar suka yaye a ƙarshen makon da ya gabata, bayan da aka basu horo na musamman don sauya ɗabi’unsu da nufin ci gaba da rayuwar fararen hula a cikin jama’a.

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne mahukuntan na Nijar suka gudanar da bikin yaye tubabbun mayaƙan na Boko Haram 124 adadin da ya ƙunshi har da ƙananan yara 44 bayan da aka basu horo kan ayyukan dogaro da kai daban-daban.

Gwamnan jihar Diffa da ke kudu maso gabashin ƙasar Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma yayin jawabinsa wajen bikin yaye tubabbun ƴan ta’addan ya ce abin farin ciki ne samun nasarar sauya ɗabi’un mutanen don mayar da su cikin fararen hula don ci gaba da rayuwa kamar kowa.

Wata sanarwa da ma’aikatar cikin gida ta fitar a Jamhuriyyar ta Nijar ta ce dukkanin tubabbun ƴan ta’addan 124 sun samu takardun shaidar kammala samun horo ta yadda ake da yaƙinin za su yi ingantacciyar rayuwa cikin fararen hula.

Wannan ne karon farko da Nijar ke yaye tubabbun mayaƙan Boko Haram tare da mayar da su cikin al’umma ko da ya ke hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Mohammed ya yi makamancin wannan yunƙurin a shekarar 2023 watanni gabanin yi masa juyin mulkin.

Tun shekarar 2017 ne tubabbun mayaƙan fiye da 700 suka ajje makamansu wanda ya bayar da damar fara yi musu horo na musamman don mayar da rayuwarsu da tunaninsu irin na sauran fararen hula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp