Home AFIRKA Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a...

Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a Nijar

Aƙalla tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 ne mahukunta Jamhuriyyar Nijar suka yaye a ƙarshen makon da ya gabata, bayan da aka basu horo na musamman don sauya ɗabi’unsu da nufin ci gaba da rayuwar fararen hula a cikin jama’a.

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne mahukuntan na Nijar suka gudanar da bikin yaye tubabbun mayaƙan na Boko Haram 124 adadin da ya ƙunshi har da ƙananan yara 44 bayan da aka basu horo kan ayyukan dogaro da kai daban-daban.

Gwamnan jihar Diffa da ke kudu maso gabashin ƙasar Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma yayin jawabinsa wajen bikin yaye tubabbun ƴan ta’addan ya ce abin farin ciki ne samun nasarar sauya ɗabi’un mutanen don mayar da su cikin fararen hula don ci gaba da rayuwa kamar kowa.

Wata sanarwa da ma’aikatar cikin gida ta fitar a Jamhuriyyar ta Nijar ta ce dukkanin tubabbun ƴan ta’addan 124 sun samu takardun shaidar kammala samun horo ta yadda ake da yaƙinin za su yi ingantacciyar rayuwa cikin fararen hula.

Wannan ne karon farko da Nijar ke yaye tubabbun mayaƙan Boko Haram tare da mayar da su cikin al’umma ko da ya ke hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Mohammed ya yi makamancin wannan yunƙurin a shekarar 2023 watanni gabanin yi masa juyin mulkin.

Tun shekarar 2017 ne tubabbun mayaƙan fiye da 700 suka ajje makamansu wanda ya bayar da damar fara yi musu horo na musamman don mayar da rayuwarsu da tunaninsu irin na sauran fararen hula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp