Home AFIRKA Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a...

Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a Nijar

Aƙalla tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 ne mahukunta Jamhuriyyar Nijar suka yaye a ƙarshen makon da ya gabata, bayan da aka basu horo na musamman don sauya ɗabi’unsu da nufin ci gaba da rayuwar fararen hula a cikin jama’a.

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne mahukuntan na Nijar suka gudanar da bikin yaye tubabbun mayaƙan na Boko Haram 124 adadin da ya ƙunshi har da ƙananan yara 44 bayan da aka basu horo kan ayyukan dogaro da kai daban-daban.

Gwamnan jihar Diffa da ke kudu maso gabashin ƙasar Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma yayin jawabinsa wajen bikin yaye tubabbun ƴan ta’addan ya ce abin farin ciki ne samun nasarar sauya ɗabi’un mutanen don mayar da su cikin fararen hula don ci gaba da rayuwa kamar kowa.

Wata sanarwa da ma’aikatar cikin gida ta fitar a Jamhuriyyar ta Nijar ta ce dukkanin tubabbun ƴan ta’addan 124 sun samu takardun shaidar kammala samun horo ta yadda ake da yaƙinin za su yi ingantacciyar rayuwa cikin fararen hula.

Wannan ne karon farko da Nijar ke yaye tubabbun mayaƙan Boko Haram tare da mayar da su cikin al’umma ko da ya ke hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Mohammed ya yi makamancin wannan yunƙurin a shekarar 2023 watanni gabanin yi masa juyin mulkin.

Tun shekarar 2017 ne tubabbun mayaƙan fiye da 700 suka ajje makamansu wanda ya bayar da damar fara yi musu horo na musamman don mayar da rayuwarsu da tunaninsu irin na sauran fararen hula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp