Home General Harin sojin saman Najeriya ya sake hallaka tarin fararen hula a Zamfara

Harin sojin saman Najeriya ya sake hallaka tarin fararen hula a Zamfara

Nigeria Airforce

Sojin saman Najeriya sun sake hallaka fararen hula aƙalla 16 yayin wasu hare-hare da suka nufaci kaiwa kan ƴan bindigar da ke ƙauyuka a ƙananan hukumomin Zurmi da Maradun na jihar Zamfara, fararen hular da bayanai ke cewa galibinsu ƴan sakai ne da suka gwabza faɗa da ƴan bindigar.

Rahotanni sun bayyana cewa tun farko ƴan sa kan da ke taimakawa wajen fatattakar ƴan bindiga a ƙauyukan ne suka nemi ɗauki don taimakawa musu wajen kammala murƙushe ƴan bindigar da suke tsaka da faɗa da su, amma kuma Sojojin saman na Najeriya suka yi tsammanin su ne ƴan bindigar inda nan ta ke suka buɗe musu wuta.

Tuni dai gwamnan jihar ta Zamfara Dauda Lawal ya aike da saƙon jaje ga iyalai da ƴan uwan ƴan sa kan da suka mutu a wannan hari yayinda ya jinjinawa Sojin na Najeriya game da namijin ƙoƙarin da suke wajen kakkaɓe barazanar ƴan bindiga a jihar.

Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta miƙa sakon ta’aziyya kan kisan ƴan sa kan waɗanda ta ce sun nuna matuƙar jajircewa a wanzar da zaman lafiya ga al’ummar ta Tungar Kara a ƙaramar hukumar Zurmi wajen kange barazanar ƴan bindigar da ke afkawa jama’a.

Rahotanni sun ce ƴan sa kan, na kan hanyarsu ta barin Gidan Makera ne na yankin Boko duk dai a ƙaramar hukumar ta Zurmi lokacin da haɗarin ya faru a yau Lahadi, da ya kai ga rasa rayukan 16 daga cikinsu.

Wannan tsautsauyi na zuwa a dai dai lokacin da wasu ƴan sa kan fiye da 30 suka rasa ransu cikin makon jiya can a jihar Katsina bayan da wani gungun ƴan bindiga ya afka musu, lamarin da ke nuna gagarumar asarar da aka fuskanta a ƙoƙarin da fararen hula ke yi na bai wa kansu kariya daga barazanar ƴan bindiga.

A cewar wasu bayanai tsautsayin ya faru ne a lokacin da Sojin saman na Najeriya ke kan hanyarsu ta dawowa daga luguden wutar da suka yi wa maɓoyar ƴan bindigar a garin na Tungar Kara yau lahadi, kwatsam kuma sai suka ci karo da ayarin ƴan sa kan dalilin ya sanya suka tsammaci cewa ƴan sa kan, wani ɓangare ne na ƴan bindigar suke ƙoƙarin guduwa.

Wannan dai ba shi ne karon farko da Sojin Najeriya ke kashe tarin fararen hula ko kuma ƴan sa kai ko ma ƴan gudun hijira bisa tsammanin kasancewarsu ƴan bindiga ko ƴan ta’adda ba.

Masana dai na alaƙanta kuskuren kisan ƴan sa kan, da yadda ake gaza musayar bayanai tsakanin irin waɗannan mutane da ke taimakawa zaman lafiyar yankuna da kuma jami’an tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp