Home General Jam’iyyar LP a Nijeriya ta zargi Tinubu kan batan wasu kudi a...

Jam’iyyar LP a Nijeriya ta zargi Tinubu kan batan wasu kudi a hukumar kidaya

Jam’iyyar adawa ta Labour a Najeriya ta zargi gwamnatin kasar da gazawa wajen yi wa ‘yan Najeriya bayani kan yadda aka yi da naira biliyan 234 wani bangare na kudin kidayar jama’a da aka shirya gudanarwa a shekara ta 2023, da aka dakatar.

Jam’iyyar na zargin cewa an karkatar da kudaden ne wajen yakin neman zaben 2023.

Jam’iyyar ta Labour ta ce a karkashin gwamnatin da ta gabata ta shugaba Muhammadu Buhari, hukumar kidayar jama’a ta kasar ta bukaci a sahale mata kashe naira biliyan 800 domin gudanar da kidayar jama’a data gidaje, to amma bayan watanni 17 shiru kake ji babu wani abu da aka yi, sannan kuma gwamnatin shugaba Bola Tinubu bata ce komai ba a kai ballantana sanar da ranar da za ayi kidayar.

Shirun da gwamnati mai ci yanzu ta yi wajen kin bayani a akan halin da ake ciki a game da batun kidayar shi ne ya janyo wannan zargi da jam’iyyar ta Labour ta yi.

Dr Yunusa Tanko, daya ne daga cikin masu magana da yawun jam’iyyar, kuma ya ce a yanzu dai shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinibu bashi da wani bayani da zai yi wa ‘yan Najeriyar kan yadda aka yi da kudaden kidiyar, saboda gazawar gwamnatinsa na sanar da ranar da za a gudanar da ita.

Ya ce “Abu ne mai kyau a gudanar da wannan kidaya domin ta haka ne za a san yawan ‘yan Najeriya dama irin abubuwan da ya kamata a yi musu, sannan kuma su wadannan kudade na gudanar da wannan kidaya tuni aka waresu, kuma har yanzu babu wani bayani a kan abin da ya hana yin kidayar, to abin tamabaya anan ina kudaden suke?”

Mai magana da yawun Peter Obin, ya ce ya kamata a fito fili a bayyanawa ‘yan Najeriya inda aka kwana a game da kidayar jama’a.

Dr Yunusa Tanko, ya ce,” Mun taso da wannan magana ne domin sanin halin da ake ciki, don yin shiru akan hakan ba dai-dai bane.”

Ya ce,” Hakkin duk wani dan Najeriya ne ya san halin da ake ciki a game da inda aka kwana a kidayar jama’a da aka shirya yi.”

A nata bangaren jam’iyya mai mulkin Najeriya APC, ta fito ta musanta dukkan zarge-zargen da jam’iyyar ta Labour ke mata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp