Home General Hajjin 2025: Gwamnatin Najeriya ta zaɓi kamfanonin jirage huɗu domin jigilar maniyyata

Hajjin 2025: Gwamnatin Najeriya ta zaɓi kamfanonin jirage huɗu domin jigilar maniyyata

Gwamnatin Najeriya ta amince da kamfanonin jiragen sama guda huɗu domin jigilar maniyyata Hajjin bana.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban hukumar jin daɗin alhazai ta Najeriya, NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce an zaɓi kamfanoni huɗu ne daga cikin guda 11 da suka nuna sha’awar aikin jigilar maniyyatan, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Ya ce kamfanonin huɗu su ne: Air Peace Ltd, da wani kamfanin ƙasar Saudiya mai suna Fly-Nas da Max Air da kuma UMZA Aviation Services Ltd.

Ya ƙara da cewa kwamiti mai mutum 32 da aka kafa a ranar 26 ga Nuwamban bara ne suka zauna suka tantance kamfanonin, kafin suka amince da guda huɗun

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp