Home General Wutar lantarkin Najeriya ta ɗauke gaba ɗaya karon farko a sabuwar shekara

Wutar lantarkin Najeriya ta ɗauke gaba ɗaya karon farko a sabuwar shekara

Najeriya ta sake tsunduma cikin duhu bayan faɗuwar babban layin samar da wutar lantarki na ƙasa, da yammacin ranar Asabar.

Wannan ɗaukewa ita ce karo na farko a shekarar 2025, amma karo na 13 cikin watanni 13 da suka gabata.

Rahotanni sun nuna cewa wutar lantarki ta fara raguwa daga megawat 2,111.01 da misalin ƙarfe 2 na rana.

Daga bisani ta sauka zuwa megawat 390.20 da misalin ƙarfe 3 na rana.

A shekarar da ta gabata, layin samar da wutar lantarkin ya lalace sau 12, wanda hakan ya jefa miliyoyin ’yan Najeriya cikin duhu tare da kawo cikas ga tattalin arziƙi da rayuwar yau da kullum.

Wannan lalacewar na zuwa ne kwanaki 11 kacal da shiga sabuwar shekarar 2025.

Hakan ya sake nuna yadda matsalar rashin ingantaccen tsarin samar da wutar lantarki ke ta’azzara a ƙasar.

Al’ummar Najeriya dai na ci gaba da fuskantar ƙalubale a fannin samar da wutar lantarki, wanda ke da matuƙar tasiri a harkokin kasuwanci, masana’antu, da rayuwar yau da kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp