Home General Wutar lantarkin Najeriya ta ɗauke gaba ɗaya karon farko a sabuwar shekara

Wutar lantarkin Najeriya ta ɗauke gaba ɗaya karon farko a sabuwar shekara

Najeriya ta sake tsunduma cikin duhu bayan faɗuwar babban layin samar da wutar lantarki na ƙasa, da yammacin ranar Asabar.

Wannan ɗaukewa ita ce karo na farko a shekarar 2025, amma karo na 13 cikin watanni 13 da suka gabata.

Rahotanni sun nuna cewa wutar lantarki ta fara raguwa daga megawat 2,111.01 da misalin ƙarfe 2 na rana.

Daga bisani ta sauka zuwa megawat 390.20 da misalin ƙarfe 3 na rana.

A shekarar da ta gabata, layin samar da wutar lantarkin ya lalace sau 12, wanda hakan ya jefa miliyoyin ’yan Najeriya cikin duhu tare da kawo cikas ga tattalin arziƙi da rayuwar yau da kullum.

Wannan lalacewar na zuwa ne kwanaki 11 kacal da shiga sabuwar shekarar 2025.

Hakan ya sake nuna yadda matsalar rashin ingantaccen tsarin samar da wutar lantarki ke ta’azzara a ƙasar.

Al’ummar Najeriya dai na ci gaba da fuskantar ƙalubale a fannin samar da wutar lantarki, wanda ke da matuƙar tasiri a harkokin kasuwanci, masana’antu, da rayuwar yau da kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp