Home General Sojoji sun ce sun lalata sansanin Bello Turji tare da kashe ‘yanbindiga...

Sojoji sun ce sun lalata sansanin Bello Turji tare da kashe ‘yanbindiga 25

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar lalata sansanin gawurtaccen ɗan bindigar nan Bello Turji a yankin Fakai na ƙaramar hukumar Shinkafi.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar da ke yaƙi da ‘yanbindiga a arewa maso yamma ‘Operation Fansan Yamma’ ya fitar, ya ce dakarun sojin sun ƙaddamar da hare-haren ne kan maɓoyar ‘yanbindigar a ranar 10 ga watan Janairu.

”Bisa taimakon dakarun sojin sama, mun samu nasarar lalata sansanonin wasu ‘yanbindiga a yankin Fakai na ƙaramar hukumar Shinkafi”, in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa daga cikin sansanonin da aka lalata har da na Bello Turji da Mallam Ila, inda aka kashe ‘yanbindiga 25 tare da raunata fiye da 18.

Haka ma ya ce a lokacin samamen sojojin sun kuɓutar da mutum bakwai da ‘yanbindigar suka yi garkuwa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp