Home General Rikicin masarautar Kano: Mun gamsu da hukuncin kotun daukaka kara ta yanke...

Rikicin masarautar Kano: Mun gamsu da hukuncin kotun daukaka kara ta yanke – Gwamnatin Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta nuna Jin dadinta da hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke dangane da batun da ya shafi Masarautar Kano na dawo Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu.

Kwamishinan shari’a na Jihar Kano Barrister Haruna Isah Dediri ya bayyana gamsuwarsa Lokacin da ya ke ganawa da manema labaru.

Dederi ya ce Hukuncin da kotun daukaka karar ta yi, ya soke hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke a baya, ya kuma tabbatar da matakin da gwamnatin Kano ta dauka dangane da nade-nade, mukamai da Kuma gyare-gyare a masarautar Kano.

”Duk wasu hukunce-hukunce da babbar kotun tarayya ta yi a baya wadanda suka shafi rikicin masarautu a Kano ya zama rusashshe, idan kai la’akari da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a jiya”. Inji Barr. Dederi

Dederi ya ce a madadin gwamnatin jihar Kano suna yabawa bangaren shari’a na kasar nan saboda yadda ya yanke hukuncin ba tare da daukar wani bangare ba, dangane da rikicin masarautu a Kano.

“Da wannan hukuncin za gwamnatin jihar Kano za ta tabbatar da cigaba da aiki kafa da kada da masarautun gargajiya domin ciyar da jihar Kano gaba ta kowacce fuska”. A cewar Kwamishinan shari’a

Daderi ya yi kira da hukumomi da ma’aikatun gwamnati da kamfanoni da Kungiyoyi da daidaikun al’umma da su tabbatar da bin umarnin da kotun daukaka kara ta yi na tabbatar da abun da gwamnatin Kano ta yi akan abun da ya shafi Masarautar Kano.

Ya ce gwamnatin Kano tana kira ga dukkanin bangarorin da abun ya shafa da su Ajiye komai su zo a hada hannu da su don cigaban jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp