Home General Rikicin masarautar Kano: Mun gamsu da hukuncin kotun daukaka kara ta yanke...

Rikicin masarautar Kano: Mun gamsu da hukuncin kotun daukaka kara ta yanke – Gwamnatin Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta nuna Jin dadinta da hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke dangane da batun da ya shafi Masarautar Kano na dawo Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu.

Kwamishinan shari’a na Jihar Kano Barrister Haruna Isah Dediri ya bayyana gamsuwarsa Lokacin da ya ke ganawa da manema labaru.

Dederi ya ce Hukuncin da kotun daukaka karar ta yi, ya soke hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke a baya, ya kuma tabbatar da matakin da gwamnatin Kano ta dauka dangane da nade-nade, mukamai da Kuma gyare-gyare a masarautar Kano.

”Duk wasu hukunce-hukunce da babbar kotun tarayya ta yi a baya wadanda suka shafi rikicin masarautu a Kano ya zama rusashshe, idan kai la’akari da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a jiya”. Inji Barr. Dederi

Dederi ya ce a madadin gwamnatin jihar Kano suna yabawa bangaren shari’a na kasar nan saboda yadda ya yanke hukuncin ba tare da daukar wani bangare ba, dangane da rikicin masarautu a Kano.

“Da wannan hukuncin za gwamnatin jihar Kano za ta tabbatar da cigaba da aiki kafa da kada da masarautun gargajiya domin ciyar da jihar Kano gaba ta kowacce fuska”. A cewar Kwamishinan shari’a

Daderi ya yi kira da hukumomi da ma’aikatun gwamnati da kamfanoni da Kungiyoyi da daidaikun al’umma da su tabbatar da bin umarnin da kotun daukaka kara ta yi na tabbatar da abun da gwamnatin Kano ta yi akan abun da ya shafi Masarautar Kano.

Ya ce gwamnatin Kano tana kira ga dukkanin bangarorin da abun ya shafa da su Ajiye komai su zo a hada hannu da su don cigaban jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp