Home General Mutune dari ne suka mutu a Najeriya dalilin gobara a shekarar 2024

Mutune dari ne suka mutu a Najeriya dalilin gobara a shekarar 2024

Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa ta bayyana cewa, Najeriya ta yi asarar rayuka mutane 100 da dukiyar da ta kai Naira biliyan 67.1 sakamakon ɓarkewar gobara a shekarar 2024.

Hukumar ta kuma ce an ceto rayuka al’umma 30,890 da kadarorin da darajarsu ta kai N1.94tr daga ɓarnar da aka samu a lokacin ɓarkewar gobara daban-daban a faɗin ƙasar nan a shekarar 2024.

Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, Abdulganiyu Jaji ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Ya ce, “A shekarar 2024, hukumar kashe gobara ta yi nasarar ceto dukiyoyin da darajarsu ta kai Naira tiriliyan 1.94 tare da yin asarar dukiyoyi da aka yi ƙiyasin ta kai ta Naira biliyan 67.1.

“A cikin wannan shekarar, Hukumar kashe gobara ta kai ɗauki kashe gobara da sauran abubuwan gaggawa inda aka ceto rayuka 30,890 yayin da mutane 23 suka rasa rayukansu. A matsayinmu na ’yan Najeriya, muna cikin waɗanda ke jajantawa iyalan waɗanda suka rasu da kuma ‘yan uwansu.”

Ya danganta yawancin abubuwan da suka faru da sakaci da rashin bin ƙa’idojin kariya.

Jaji ya buƙaci ‘yan Najeriya da su ƙara taka tsantsan a lokacin bazara, inda ya ƙara da cewa haɗarin gobara yana da yawa a wannan kakar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp