Home General Mutune dari ne suka mutu a Najeriya dalilin gobara a shekarar 2024

Mutune dari ne suka mutu a Najeriya dalilin gobara a shekarar 2024

Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa ta bayyana cewa, Najeriya ta yi asarar rayuka mutane 100 da dukiyar da ta kai Naira biliyan 67.1 sakamakon ɓarkewar gobara a shekarar 2024.

Hukumar ta kuma ce an ceto rayuka al’umma 30,890 da kadarorin da darajarsu ta kai N1.94tr daga ɓarnar da aka samu a lokacin ɓarkewar gobara daban-daban a faɗin ƙasar nan a shekarar 2024.

Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, Abdulganiyu Jaji ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Ya ce, “A shekarar 2024, hukumar kashe gobara ta yi nasarar ceto dukiyoyin da darajarsu ta kai Naira tiriliyan 1.94 tare da yin asarar dukiyoyi da aka yi ƙiyasin ta kai ta Naira biliyan 67.1.

“A cikin wannan shekarar, Hukumar kashe gobara ta kai ɗauki kashe gobara da sauran abubuwan gaggawa inda aka ceto rayuka 30,890 yayin da mutane 23 suka rasa rayukansu. A matsayinmu na ’yan Najeriya, muna cikin waɗanda ke jajantawa iyalan waɗanda suka rasu da kuma ‘yan uwansu.”

Ya danganta yawancin abubuwan da suka faru da sakaci da rashin bin ƙa’idojin kariya.

Jaji ya buƙaci ‘yan Najeriya da su ƙara taka tsantsan a lokacin bazara, inda ya ƙara da cewa haɗarin gobara yana da yawa a wannan kakar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp